ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Damu Matuka Kan Ta’azzarar Rikici Da Tasirinsa Kan Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya bayyana a yayin taron manema labaru na yau da kullum Alhamis din nan cewa, kasar Sin tana bakin ciki matuka da yadda rikicin da ke faruwa a halin yanzu tsakanin Palasdinu da Isra’ila, ya haifar da hasarar rayukan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba, tare da nuna matukar damuwa game da tabarbarewar yanayin tsaro da ma jin kai a yankin Falasdinu, ta kuma damu matuka game da mummunan tasirin da tashin hankalin zai haifar ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Wang Wenbin ya bayyana cewa, kasar Sin ta lura cewa, kungiyar hadin kan kasashen Larabawa ta gudanar da taron gaggawa na ministocin harkokin wajen kungiyar, inda ta zartas da wani kuduri dake goyon bayan kungiyar wajen taka muhimmiyar rawa kan batun Palasdinu.

  • Shugaba Xi Ya Yi Rangadi A Biranen Jingdezhen Da Shangrao Na Lardin Jiangxi 
  • Kungiyar Kasashen Larabawa Ta Yi Taro Kan Rikicin Isra’ila da Falasdinu

Kasar Sin da kasashen Larabawa na da kusan ra’ayi daya kan batun Falasdinu, inda bangarorin biyu suka yi kira da a hanzarta tsagaita bude wuta da kawo karshen hare-haren bama-bamai, da yin Allah wadai da ayyukan dake cutar da fararen hula, da kaucewa ta’azzarar al’amura da haddasa bala’in jin kai.

ADVERTISEMENT

Wang Wenbin ya ce, kasar Sin tana son ci gaba da yin mu’amala da hadin gwiwa tare da dukkan bangarorin kungiyar hadin kan kasashen Larabawa, da sa kaimi ga yin shawarwarin zaman lafiya, da kokarin maido da shirin zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya kan turba mai kyau.

Bugu da kari, a jiya manzon musamman na kasar Sin kan batun Gabas ta tsakiya Mr. Zhai Jun ya tattauna kan yanayin da Palestinu da Isra’ila ke ciki tare da mataimakiyar ministan harkokin wajen kasar Palestinu ta farko Amal Jadou ta wayar tarho, inda Zhai Jun ya bayyana cewa, kasar Sin ta damu matuka da rasuwar fararen hula da dama sakamakon rikicin Palestinu da Isra’ila.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Ya kara da cewa, yanzu abu mafi muhimmanci shi ne, a tsaigaita bude wuta nan take. Kuma kamata ya yi kasashen duniya su yi kokari domin sassauta rikicin, tare kuma da samar da taimakon jin kai ga al’ummar Palestinu. Ya ce kasar Sin za ta ci gaba da yin kokari domin cimma burin tsagaita bude wuta tsakanin sassan biyu, tare kuma da samar da tallafi domin sassauta rikicin jin kai, kana za ta ci gaba da shawo kan sassan biyu, su komawa shawarwarin wanzar da zaman lafiya, ta yadda za a daidaita batun Palestinu bisa adalci daga duk fannoni.

A na ta bangare, Jadou ta gode wa kasar Sin bisa matsayin adalcin da take kai game da batun Palestinu. A cewarta, Palestinu ta na da cikakken imani da kasar Sin, kuma tana fatan kasar Sin za ta ci gaba da taka rawar gani kan batun a halin da ake ciki yanzu. (Mai fassara: Ibrahim Yaya, Jamila Zhou)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kasance Mai Asali Daga Sin Amma Mai Rungumar Dukkanin Duniya

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kasance Mai Asali Daga Sin Amma Mai Rungumar Dukkanin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.