• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwar Shanu: ‘Yan Arewa Sun Koka Da Barazanar Korar Su A Abiya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Kasuwar Shanu: ‘Yan Arewa Sun Koka Da Barazanar Korar Su A Abiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabannin kungiyar ‘yan kasuwan arewa da ke kasuwar shanu ta Lobbanta Garke a karamar hukumar Umunneochi cikin Jihar Abiya sun bukaci Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da mai alfarma sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar ll su saka baki game da wa’adin kwanaki 14 da gwamnatin Abiya ta ba su na su fice daga kasuwar.

Mataimakin shugaban ‘yan kungiyar kasuwan shanu ta Lobbanta, Buba Abdullahi Kedemure shi ne ya jagoranci sauran shugabannin zuwa ofishin kungiyar tuntuba ta kasa (NCM) da ke Kaduna, wanda suka ce sun zo mika kokensu ne kan wa’adin korar da gwamnatin Jihar Abiya ta ba su na ficewa daga kasuwar.

  • Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Nijeriya Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci?
  • An Horas Da Makiyaya Dabarun Shuka Ciyawar Shanu A Kaduna

Mataimakin shugaban kungiyar ya kara da cewa sun ‘yan kasa nagari masu bin doka wajen gudanar da harkokin kasuwancinsu a tsawon shekaru masu yawa a cikin jihar, amma a yanzu an ba su wa’adin ficewa daga kasuwan kan zargin aika-ta ta’addanci wanda suka musanta.

“Muna rokon shugabanninmu da su saka baki tare da yin kira ga gwamnan domin janye wa’adin na kwanaki 14 da aka ba mu na ficewa daga kasuwan,” in ji shi.

Shugaban kungiyar tuntuba na arewa, Dakta Auwal Abdullahi ya bayyana kudurinsa na daukan mataki a daidai lokacin da ‘yan kasuwar arewa ke fuskantar wulakanci a Abiya ko wani bangare na jihohin gabashin Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Ya tunatar da gwamnatin Jihar Abiya da sauran gwamnonin kudu maso gabas ce-wa ‘yan kabilar Igbo na gudanar da harkokin kasuwancinsu na biliyoyin naira a jihohin Kaduna da Kano da Katsina da ma sauran jihohin Arewa amma ba sa fus-kantar wata tsangwama.

Auwal ya ce babban aikinsu shi ne kare muradun Arewa da ‘yan Arewa bisa tsarin doka. Don haka ya yi kira ga gwamnan Jihar Abiya da ya janye wa’adin kwanaki 14 da ya bai wa ‘yan Arewa masu gudanar da sana’o’i na halal a kasuwar shanu ta Garke a jihar.

Da yake mayar da martani game da lamarin, mai bai wa gwamnan shawara na musamman kan harkokin tsaro, MacDonald Ubah, wanda ya yi jawabi ga mane-ma labarai a ranar Litinin a Umuahia, ya yi watsi da jita-jita a matsayin karyar zance mara tushe.

Ya zargi masu yada wannan jita-jita da karkatar da umarnin gaskiya da gwamnati ta bayar domin haifar da rudani da bata wa Gwamna Aled Otti suna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasuwar hatsiKiwon shano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Jaddada Jan Hankalin Ma’aikata Da Su Shiga Aikin Farfado Da Kasa

Next Post

CMG Ya Rattaba Hannu Tare Da Kawancen LFP Na Faransa Kan Takardar Bayanin Hadin-Gwiwa

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

36 minutes ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

2 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

3 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

4 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

6 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

6 hours ago
Next Post
CMG Ya Rattaba Hannu Tare Da Kawancen LFP Na Faransa Kan Takardar Bayanin Hadin-Gwiwa

CMG Ya Rattaba Hannu Tare Da Kawancen LFP Na Faransa Kan Takardar Bayanin Hadin-Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.