• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwar Shanu: ‘Yan Arewa Sun Koka Da Barazanar Korar Su A Abiya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Kasuwar Shanu: ‘Yan Arewa Sun Koka Da Barazanar Korar Su A Abiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabannin kungiyar ‘yan kasuwan arewa da ke kasuwar shanu ta Lobbanta Garke a karamar hukumar Umunneochi cikin Jihar Abiya sun bukaci Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da mai alfarma sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar ll su saka baki game da wa’adin kwanaki 14 da gwamnatin Abiya ta ba su na su fice daga kasuwar.

Mataimakin shugaban ‘yan kungiyar kasuwan shanu ta Lobbanta, Buba Abdullahi Kedemure shi ne ya jagoranci sauran shugabannin zuwa ofishin kungiyar tuntuba ta kasa (NCM) da ke Kaduna, wanda suka ce sun zo mika kokensu ne kan wa’adin korar da gwamnatin Jihar Abiya ta ba su na ficewa daga kasuwar.

  • Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Nijeriya Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci?
  • An Horas Da Makiyaya Dabarun Shuka Ciyawar Shanu A Kaduna

Mataimakin shugaban kungiyar ya kara da cewa sun ‘yan kasa nagari masu bin doka wajen gudanar da harkokin kasuwancinsu a tsawon shekaru masu yawa a cikin jihar, amma a yanzu an ba su wa’adin ficewa daga kasuwan kan zargin aika-ta ta’addanci wanda suka musanta.

“Muna rokon shugabanninmu da su saka baki tare da yin kira ga gwamnan domin janye wa’adin na kwanaki 14 da aka ba mu na ficewa daga kasuwan,” in ji shi.

Shugaban kungiyar tuntuba na arewa, Dakta Auwal Abdullahi ya bayyana kudurinsa na daukan mataki a daidai lokacin da ‘yan kasuwar arewa ke fuskantar wulakanci a Abiya ko wani bangare na jihohin gabashin Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Ya tunatar da gwamnatin Jihar Abiya da sauran gwamnonin kudu maso gabas ce-wa ‘yan kabilar Igbo na gudanar da harkokin kasuwancinsu na biliyoyin naira a jihohin Kaduna da Kano da Katsina da ma sauran jihohin Arewa amma ba sa fus-kantar wata tsangwama.

Auwal ya ce babban aikinsu shi ne kare muradun Arewa da ‘yan Arewa bisa tsarin doka. Don haka ya yi kira ga gwamnan Jihar Abiya da ya janye wa’adin kwanaki 14 da ya bai wa ‘yan Arewa masu gudanar da sana’o’i na halal a kasuwar shanu ta Garke a jihar.

Da yake mayar da martani game da lamarin, mai bai wa gwamnan shawara na musamman kan harkokin tsaro, MacDonald Ubah, wanda ya yi jawabi ga mane-ma labarai a ranar Litinin a Umuahia, ya yi watsi da jita-jita a matsayin karyar zance mara tushe.

Ya zargi masu yada wannan jita-jita da karkatar da umarnin gaskiya da gwamnati ta bayar domin haifar da rudani da bata wa Gwamna Aled Otti suna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasuwar hatsiKiwon shano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Jaddada Jan Hankalin Ma’aikata Da Su Shiga Aikin Farfado Da Kasa

Next Post

CMG Ya Rattaba Hannu Tare Da Kawancen LFP Na Faransa Kan Takardar Bayanin Hadin-Gwiwa

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

4 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

5 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

11 hours ago
Shanu
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

11 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

12 hours ago
Next Post
CMG Ya Rattaba Hannu Tare Da Kawancen LFP Na Faransa Kan Takardar Bayanin Hadin-Gwiwa

CMG Ya Rattaba Hannu Tare Da Kawancen LFP Na Faransa Kan Takardar Bayanin Hadin-Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.