ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwar Shanu: ‘Yan Arewa Sun Koka Da Barazanar Korar Su A Abiya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Shanu

Shugabannin kungiyar ‘yan kasuwan arewa da ke kasuwar shanu ta Lobbanta Garke a karamar hukumar Umunneochi cikin Jihar Abiya sun bukaci Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da mai alfarma sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar ll su saka baki game da wa’adin kwanaki 14 da gwamnatin Abiya ta ba su na su fice daga kasuwar.

Mataimakin shugaban ‘yan kungiyar kasuwan shanu ta Lobbanta, Buba Abdullahi Kedemure shi ne ya jagoranci sauran shugabannin zuwa ofishin kungiyar tuntuba ta kasa (NCM) da ke Kaduna, wanda suka ce sun zo mika kokensu ne kan wa’adin korar da gwamnatin Jihar Abiya ta ba su na ficewa daga kasuwar.

  • Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Nijeriya Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci?
  • An Horas Da Makiyaya Dabarun Shuka Ciyawar Shanu A Kaduna

Mataimakin shugaban kungiyar ya kara da cewa sun ‘yan kasa nagari masu bin doka wajen gudanar da harkokin kasuwancinsu a tsawon shekaru masu yawa a cikin jihar, amma a yanzu an ba su wa’adin ficewa daga kasuwan kan zargin aika-ta ta’addanci wanda suka musanta.

ADVERTISEMENT

“Muna rokon shugabanninmu da su saka baki tare da yin kira ga gwamnan domin janye wa’adin na kwanaki 14 da aka ba mu na ficewa daga kasuwan,” in ji shi.

Shugaban kungiyar tuntuba na arewa, Dakta Auwal Abdullahi ya bayyana kudurinsa na daukan mataki a daidai lokacin da ‘yan kasuwar arewa ke fuskantar wulakanci a Abiya ko wani bangare na jihohin gabashin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Ya tunatar da gwamnatin Jihar Abiya da sauran gwamnonin kudu maso gabas ce-wa ‘yan kabilar Igbo na gudanar da harkokin kasuwancinsu na biliyoyin naira a jihohin Kaduna da Kano da Katsina da ma sauran jihohin Arewa amma ba sa fus-kantar wata tsangwama.

Auwal ya ce babban aikinsu shi ne kare muradun Arewa da ‘yan Arewa bisa tsarin doka. Don haka ya yi kira ga gwamnan Jihar Abiya da ya janye wa’adin kwanaki 14 da ya bai wa ‘yan Arewa masu gudanar da sana’o’i na halal a kasuwar shanu ta Garke a jihar.

Da yake mayar da martani game da lamarin, mai bai wa gwamnan shawara na musamman kan harkokin tsaro, MacDonald Ubah, wanda ya yi jawabi ga mane-ma labarai a ranar Litinin a Umuahia, ya yi watsi da jita-jita a matsayin karyar zance mara tushe.

Ya zargi masu yada wannan jita-jita da karkatar da umarnin gaskiya da gwamnati ta bayar domin haifar da rudani da bata wa Gwamna Aled Otti suna.

Shanu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya
Labarai

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Next Post
CMG Ya Rattaba Hannu Tare Da Kawancen LFP Na Faransa Kan Takardar Bayanin Hadin-Gwiwa

CMG Ya Rattaba Hannu Tare Da Kawancen LFP Na Faransa Kan Takardar Bayanin Hadin-Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.