• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Bunƙasa Ilmi A Kano: Yadda Gwamnatin Abba Gida-gida Ta Tura Dalibai 1001 Karatu Kasashen Waje

by Sulaiman
2 years ago
Kano

A ƙoƙarin ta daukaka darajar ilmi, Gwamnatin Jihar Kano ta zaɓi ɗalibai 1001 da ta fara ɗaukar nauyin karatunsu a digiri na biyu a ƙasashen waje.

An rahoto cewa, daga cikin Daliban akwai wadanda aka tura zuwa Jami’o’in kasar Indiya wasu kuma zuwa Jami’o’in Kasar Uganda domin samun ilimi a fanni daban-daban.

  • Dage Takunkumin CBN A Asusun Ajiyar Wasu Mutane Da Kamfanoni Ya Haifar Da Da Mai Ido
  • Zaben 2023: Takaddamar Kashi 94 Cikin 100 Na Kujerun Da Aka Lashe Ta Dora Shakku Kan INEC

Gwamna Abba Kabir Yusuf, wanda ya rage kuɗin rajistar shiga jami’a da na zangon karatu da kashi 50 bisa 100 a kwanan baya, ya ƙaddamar da Shirin Bada Tallafin Karatu a Ƙasashen Waje, wanda aka fara ranar Alhamis da jigilar ɗalibai 550 daga Kano.

Gwamna Kabir ya ce, ya ɗora wannan gagarimin aikin alheri ne daga inda tsohon Gwamnan Kano, kuma madugun Kwankwasiyya, Rabi’u Kwankwaso ya tsaya, a lokacin mulkinsa.

Kano

LABARAI MASU NASABA

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Ya ce ayyukan alherin da gwamnatin Kwankwaso ta yi wa al’ummar Kano a baya, su na da muhimmancin da ba za a iya daina ci gaba da su ba.

Kabir ya ce, ga shi nan ƙarara ana ta cin moriya da amfanar waɗanda suka je waje karatu a ƙarƙashin gwamnatin Kwankwaso, inda wasu na riƙe da muƙamai sosai a gwamnati da sauran fannonin ayyukan yau da kullum.

Ya lissafa wasu da suka haɗa da Kwamishinan Ilmi Mai Zurfi, Dakta Yusuf Ibrahim, Shugaban Sashen Ƙididdigar Alƙaluma na Jihar Kano, Farfesa Aliyu Isa Aliyu da Mashawarci na Musamman a Fannin Ƙirƙire-ƙirƙire, Dakta Bashir Muzakkir da sauran su.

Gwamnan ya ce, “Bari na bayyana cewa, shi wannan shirin tallafin gurbin karatun waje, madugun mu Sanata Rabi’u Kwankwaso ne ya ƙirƙiro shi.”

Ya ce Kwankwaso sai da ya ɗauki nauyin rukuni-rukunin ɗalibai har rukuni uku zuwa ƙasashe 16 daban-daban.

“Wannan ƙoƙari ya sa an samu nasarar samar da daktoci, masu digiri na biyu da dubban ƙwararrun likitoci, injiniyoyi, matuƙa jirgin sama da gwanayen ayyukan harkokin jiragen ruwa da sauran su.

A jawabin sa tun da farko, Kwankwaso ya gode wa wannan gwamnati ta Abba Kabir, ganin yadda ta ci gaba da ayyukan alherin da ya fara a lokacin ya na Gwamnan Kano.

Kano

Ya ja kunnen ɗaliban su kasance masu ɗa’a kuma jakadun Kano da Nijeriya nagari a duk inda suka samu kan su.

Ɗaliban da dama sun gode wa Gwamnatin Kano, Gwamna Abba da kuma Kwankwaso.

Kafin tashinsu sai da Gwamna Abba Kabir ya damƙa wa kowa kuɗaɗen alawus ɗin sa na daloli a hannu, aka kira su taron dina a Gidan Gwamnati, sannan kuma Gwamna da Kwankwaso suka raka su har cikin jirgi.

Abba da Kwankwaso ba su bar filin jirgin Malam Aminu Kano ba, sai da suka ga tashin jirgin da ya ɗauki ɗaliban.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Next Post
Ina Fatan Fim Ya Yi Sanadiyyar Shiga Ta Gidan Aljanna – Sadiq Sani Sadiq

Ina Fatan Fim Ya Yi Sanadiyyar Shiga Ta Gidan Aljanna - Sadiq Sani Sadiq

LABARAI MASU NASABA

Kano

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.