• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Yaukaka Kawance Karkashin Dandalin FOCAC

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Yaukaka Kawance Karkashin Dandalin FOCAC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da kasar Sin ke kara cika alkawuranta na fadada kawance da sauran sassan duniya, da burin kafa al’ummar duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, yanzu haka Sin din na kara dukufa wajen yaukaka kawance, musamman ma da abokan tafiyarta, wato kasashe masu tasowa. Tuni kasar Sin ta sha alwashin ci gaba da goyon baya, da amincewar juna tsakaninta da kasashen nahiyar Afirka, wadanda suka jima da zama abokan cimma moriya tare.

Yanzu haka dai sassan biyu na aiki tukuru, wajen karfafa hadin gwiwa a fannonin kirkire-kirkire, da wanzar da zaman lafiya da daidaito, da ingiza musayar al’adu, da sauransu.

  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-17 Dauke Da ’Yan Sama Jannati
  • Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana

Karkashin hakan ne ma a baya bayan nan, kasar Sin ke kara azamar gudanar da ayyukan da suka kamata, na share fagen gudanar da dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC, wanda zai gudana cikin shekarar 2024 dake tafe.

Tuni dai jagarorin kasashen Afirka suka yi na’am da wannan dandali, wanda karkashinsa sassan biyu ke aiki tukuru, wajen cimma burikansu na bunkasuwa bisa halin da suke ciki. Har ma a baya bayan nan aka jiyo mashawarcin shugaban kasar Senegal kan harkokin diflomasiyya mista Oumar Demba Ba, na jinjinawa kasar Sin bisa himmar ta wajen kafa wannan dandali na FOCAC, wanda ya ba da babbar gudummawar ingiza kawancen Afirka da Sin bisa mutunta juna, da kyautata abota, da amincewar juna da cimma moriya tare.

Ko shakka babu dandalin FOCAC ya dunkule sassan biyu, ya kuma samar da managarcin tsarin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka.

Labarai Masu Nasaba

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

A gabar da ake dakon zagayowar lokacin gudanar da wannan muhimmin dandali, masharhanta na kara jinjinawa mashirya FOCAC bisa zurfin tunaninsu, wanda ya haifar da kafuwar sahihiyar dama ta tsara shirye-shirye, da manufofi na ingiza alakar diflomasiyya, da cinikayya, da tsaro, da hada hadar zuba jari, da kiwon lafiya, da yada ilimi da bincike, da musayar kwarewa da sanin makamar aiki, da sauran muhimman fannoni na ci gaban rayuwar bil Adama.

Fatan da duk mai burin ci gaban kasashe masu tasowa ke yi a wannan gaba, shi ne ganin bunkasar wannan dandalin na FOCAC, ta yadda zai ci gaba da dorewa bisa manufofinsa na alheri, masu yaukaka zumunta da haifar da gajiya ga kowa. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaIranSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban CMG Ya Gana Da Shugaban Dandalin Tattauna Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

CMG Da WIPO Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

Related

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare
Daga Birnin Sin

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

11 hours ago
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243
Daga Birnin Sin

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

12 hours ago
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

12 hours ago
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

14 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

15 hours ago
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

1 day ago
Next Post
CMG Da WIPO Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

CMG Da WIPO Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

October 6, 2025
Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.