ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Yaukaka Kawance Karkashin Dandalin FOCAC

by CGTN Hausa
3 years ago
FOCAC

Yayin da kasar Sin ke kara cika alkawuranta na fadada kawance da sauran sassan duniya, da burin kafa al’ummar duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, yanzu haka Sin din na kara dukufa wajen yaukaka kawance, musamman ma da abokan tafiyarta, wato kasashe masu tasowa. Tuni kasar Sin ta sha alwashin ci gaba da goyon baya, da amincewar juna tsakaninta da kasashen nahiyar Afirka, wadanda suka jima da zama abokan cimma moriya tare.

Yanzu haka dai sassan biyu na aiki tukuru, wajen karfafa hadin gwiwa a fannonin kirkire-kirkire, da wanzar da zaman lafiya da daidaito, da ingiza musayar al’adu, da sauransu.

  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-17 Dauke Da ’Yan Sama Jannati
  • Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana

Karkashin hakan ne ma a baya bayan nan, kasar Sin ke kara azamar gudanar da ayyukan da suka kamata, na share fagen gudanar da dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC, wanda zai gudana cikin shekarar 2024 dake tafe.

ADVERTISEMENT

Tuni dai jagarorin kasashen Afirka suka yi na’am da wannan dandali, wanda karkashinsa sassan biyu ke aiki tukuru, wajen cimma burikansu na bunkasuwa bisa halin da suke ciki. Har ma a baya bayan nan aka jiyo mashawarcin shugaban kasar Senegal kan harkokin diflomasiyya mista Oumar Demba Ba, na jinjinawa kasar Sin bisa himmar ta wajen kafa wannan dandali na FOCAC, wanda ya ba da babbar gudummawar ingiza kawancen Afirka da Sin bisa mutunta juna, da kyautata abota, da amincewar juna da cimma moriya tare.

Ko shakka babu dandalin FOCAC ya dunkule sassan biyu, ya kuma samar da managarcin tsarin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

A gabar da ake dakon zagayowar lokacin gudanar da wannan muhimmin dandali, masharhanta na kara jinjinawa mashirya FOCAC bisa zurfin tunaninsu, wanda ya haifar da kafuwar sahihiyar dama ta tsara shirye-shirye, da manufofi na ingiza alakar diflomasiyya, da cinikayya, da tsaro, da hada hadar zuba jari, da kiwon lafiya, da yada ilimi da bincike, da musayar kwarewa da sanin makamar aiki, da sauran muhimman fannoni na ci gaban rayuwar bil Adama.

Fatan da duk mai burin ci gaban kasashe masu tasowa ke yi a wannan gaba, shi ne ganin bunkasar wannan dandalin na FOCAC, ta yadda zai ci gaba da dorewa bisa manufofinsa na alheri, masu yaukaka zumunta da haifar da gajiya ga kowa. (Saminu Alhassan)

FOCAC
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

MASU ALAKA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Next Post
CMG Da WIPO Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

CMG Da WIPO Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
FOCAC

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
FOCAC

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.