ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Yaukaka Kawance Karkashin Dandalin FOCAC

by CGTN Hausa
3 years ago
FOCAC

Yayin da kasar Sin ke kara cika alkawuranta na fadada kawance da sauran sassan duniya, da burin kafa al’ummar duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, yanzu haka Sin din na kara dukufa wajen yaukaka kawance, musamman ma da abokan tafiyarta, wato kasashe masu tasowa. Tuni kasar Sin ta sha alwashin ci gaba da goyon baya, da amincewar juna tsakaninta da kasashen nahiyar Afirka, wadanda suka jima da zama abokan cimma moriya tare.

Yanzu haka dai sassan biyu na aiki tukuru, wajen karfafa hadin gwiwa a fannonin kirkire-kirkire, da wanzar da zaman lafiya da daidaito, da ingiza musayar al’adu, da sauransu.

  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-17 Dauke Da ’Yan Sama Jannati
  • Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana

Karkashin hakan ne ma a baya bayan nan, kasar Sin ke kara azamar gudanar da ayyukan da suka kamata, na share fagen gudanar da dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC, wanda zai gudana cikin shekarar 2024 dake tafe.

ADVERTISEMENT

Tuni dai jagarorin kasashen Afirka suka yi na’am da wannan dandali, wanda karkashinsa sassan biyu ke aiki tukuru, wajen cimma burikansu na bunkasuwa bisa halin da suke ciki. Har ma a baya bayan nan aka jiyo mashawarcin shugaban kasar Senegal kan harkokin diflomasiyya mista Oumar Demba Ba, na jinjinawa kasar Sin bisa himmar ta wajen kafa wannan dandali na FOCAC, wanda ya ba da babbar gudummawar ingiza kawancen Afirka da Sin bisa mutunta juna, da kyautata abota, da amincewar juna da cimma moriya tare.

Ko shakka babu dandalin FOCAC ya dunkule sassan biyu, ya kuma samar da managarcin tsarin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

A gabar da ake dakon zagayowar lokacin gudanar da wannan muhimmin dandali, masharhanta na kara jinjinawa mashirya FOCAC bisa zurfin tunaninsu, wanda ya haifar da kafuwar sahihiyar dama ta tsara shirye-shirye, da manufofi na ingiza alakar diflomasiyya, da cinikayya, da tsaro, da hada hadar zuba jari, da kiwon lafiya, da yada ilimi da bincike, da musayar kwarewa da sanin makamar aiki, da sauran muhimman fannoni na ci gaban rayuwar bil Adama.

Fatan da duk mai burin ci gaban kasashe masu tasowa ke yi a wannan gaba, shi ne ganin bunkasar wannan dandalin na FOCAC, ta yadda zai ci gaba da dorewa bisa manufofinsa na alheri, masu yaukaka zumunta da haifar da gajiya ga kowa. (Saminu Alhassan)

FOCAC
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

MASU ALAKA

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
Daga Birnin Sin

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Next Post
CMG Da WIPO Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

CMG Da WIPO Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.