• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Dogara Ne Kan Gaskiya Da Adalci, Za Ta Kuma Ba Da Karin Taimakon Jin Kai Zuwa Gaza

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A yau Alhamis 26 ga wata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta jaddada cewa, matsayin da kasarta ta dauka ya dogara ne kan gaskiya da adalci, kuma yana mai da martani da kakkausar murya ta kasa da kasa, musamman ma ta kasashen Larabawa.

Jami’ar ta bayyana haka ne a yayin da take amsa tambayar da aka yi kan kin amincewar da kasar Sin ta yi game da daftarin kudurin halin da Falasdinu da Isra’ila ke ciki a kwamitin sulhu na MDD.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka
  • UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

Jami’ar ta nuna cewa, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Zhang Jun, ya riga ya yi karin haske kan matsayin kasar Sin a dukkan fannoni a jawabin da ya gabatar bayan kada kuri’a a kwamitin sulhu na MDD. Jami’ar ta kuma jaddada cewa, kasar Sin ba ta da wani muradi na son kai kan batun Falasdinu. Kasar Sin tana goyon bayan duk abin da zai taimaka wajen samar da zaman lafiya, kuma za ta yi iyakacin kokarinta wajen yin sulhu tsakanin Falasdinu da Isra’ila.

A ranar 25 ga watan Oktoba, kasashen Rasha da Sin sun yi watsi da daftarin kudurin kwamitin sulhu na MDD kan halin da ake ciki tsakanin Falasdinu da Isra’ila da Amurka ta tsara, sannan Hadaddiyar Daular Larabawa ita ma ta kada kuri’ar kin amincewa da shi. Baya ga haka, sakamakon adawar da kasashen Amurka da Birtaniya da wasu kasashe suka yi, ba a amince da daftarin kudirin da Rasha ta tsara ba.

Bugu da kari, kakakin hukumar kula da hadin gwiwar ci gaban kasa da kasa ta kasar Sin Xu Wei ya bayyana a yau Alhamis cewa, gwamnatin kasar Sin za ta sake ba da wani rukunin agajin gaggawa na Yuan miliyan 15 kwatankwacin dalar Amurka Miliyan 2.05, da suka hada da abinci da magunguna ga Gaza.

LABARAI MASU NASABA

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Xu ya kara da ce, kasar Sin tana bakin cikin ganin yadda rikicin Falasdinu da Isra’ila ya haifar da hasarar rayukan fararen hula da dama da kuma tabarbarewar yanayin jin kai a Gaza.

Ya kara da cewa, don taimakawa wajen shawo kan matsalar jin kai a Gaza, kasar Sin ta riga ta ba da tsabar kudi dalar Amurka miliyan 1 ta hannun hukumar ba da agaji ta MDD mai kula da ‘yan gudun hijirar Falasdinu a gabas ta kusa da kuma hukumar Falasdinawa a lokuta daban-daban.

(Mai fassara: Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin
Daga Birnin Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas
Daga Birnin Sin

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Next Post
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kare Ci Gaban Mata A Duniya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kare Ci Gaban Mata A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.