ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Dogara Ne Kan Gaskiya Da Adalci, Za Ta Kuma Ba Da Karin Taimakon Jin Kai Zuwa Gaza

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

A yau Alhamis 26 ga wata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta jaddada cewa, matsayin da kasarta ta dauka ya dogara ne kan gaskiya da adalci, kuma yana mai da martani da kakkausar murya ta kasa da kasa, musamman ma ta kasashen Larabawa.

Jami’ar ta bayyana haka ne a yayin da take amsa tambayar da aka yi kan kin amincewar da kasar Sin ta yi game da daftarin kudurin halin da Falasdinu da Isra’ila ke ciki a kwamitin sulhu na MDD.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka
  • UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

Jami’ar ta nuna cewa, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Zhang Jun, ya riga ya yi karin haske kan matsayin kasar Sin a dukkan fannoni a jawabin da ya gabatar bayan kada kuri’a a kwamitin sulhu na MDD. Jami’ar ta kuma jaddada cewa, kasar Sin ba ta da wani muradi na son kai kan batun Falasdinu. Kasar Sin tana goyon bayan duk abin da zai taimaka wajen samar da zaman lafiya, kuma za ta yi iyakacin kokarinta wajen yin sulhu tsakanin Falasdinu da Isra’ila.

ADVERTISEMENT

A ranar 25 ga watan Oktoba, kasashen Rasha da Sin sun yi watsi da daftarin kudurin kwamitin sulhu na MDD kan halin da ake ciki tsakanin Falasdinu da Isra’ila da Amurka ta tsara, sannan Hadaddiyar Daular Larabawa ita ma ta kada kuri’ar kin amincewa da shi. Baya ga haka, sakamakon adawar da kasashen Amurka da Birtaniya da wasu kasashe suka yi, ba a amince da daftarin kudirin da Rasha ta tsara ba.

Bugu da kari, kakakin hukumar kula da hadin gwiwar ci gaban kasa da kasa ta kasar Sin Xu Wei ya bayyana a yau Alhamis cewa, gwamnatin kasar Sin za ta sake ba da wani rukunin agajin gaggawa na Yuan miliyan 15 kwatankwacin dalar Amurka Miliyan 2.05, da suka hada da abinci da magunguna ga Gaza.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Xu ya kara da ce, kasar Sin tana bakin cikin ganin yadda rikicin Falasdinu da Isra’ila ya haifar da hasarar rayukan fararen hula da dama da kuma tabarbarewar yanayin jin kai a Gaza.

Ya kara da cewa, don taimakawa wajen shawo kan matsalar jin kai a Gaza, kasar Sin ta riga ta ba da tsabar kudi dalar Amurka miliyan 1 ta hannun hukumar ba da agaji ta MDD mai kula da ‘yan gudun hijirar Falasdinu a gabas ta kusa da kuma hukumar Falasdinawa a lokuta daban-daban.

(Mai fassara: Bilkisu Xin)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kare Ci Gaban Mata A Duniya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kare Ci Gaban Mata A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Sin

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.