• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Mallaka Wa Rundujar Sojin Sama Fili Sama Da Hekta 43 Don Gina Gidaje

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Uba sani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kaduna, Mai Girma Sanata Uba Sani a ranar 25 ga Oktoba, 2023 ya mika wa Shugaban Rundunar Sojin Sama (CAS), Air Marshal Hasan Abubakar takardun mallakar fili mai fadin hekta 43.746 da Jihar Kaduna ta ware wa Rundunar Sojojin Saman Nijeriya (NAF).

A sanarwar da Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Kaduna, Muhammad Lawal Shehu ya fitar, ta ce, an tanadi Filayen ne don gina jerin gidaje da manyan jami’an Rundunar NAF zasu amfana bayan sun ajiye aiki.

  • An Dawo Da Zirga-zirgar Jiragen Sama A Filin Jirgin Sama Na Kaduna
  • Gwamnati Ta Samo Jarin Fiye Da Dala Biliyan 2 A Bangaren Wutar Lantarki

Samuel Aruwan, Shugaban Hukumar Babban Birnin Kaduna (KCTA) wanda ya wakilci Gwamna Sani a wajen taron mika takardar filin a hedikwatar NAF da ke Abuja, ya mika takardun filin ne ga shugaban sojin rundunar sama ta Nijeriya.

Gwamna Sani ya yabawa CAS bisa jagorancin sa da kuma rundunar NAF bisa kokari da sadaukarwa wajen ci gaba da yaki da ta’addanci da ‘yan fashin daji da masu garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka a jihar Kaduna da ma kasa baki daya.

Aruwan, wanda kuma shi ne mai kula da ma’aikatar tsaron cikin gida da harkokin cikin gida, ya tabbatar wa NAF kudirin gwamnatin jihar wajen inganta jin dadin ma’aikatan NAF da ma jami’an tsaro baki daya.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

 

A nasa jawabin, CAS Hassan Abubakar ya yabawa Gwamna Sani da mutanen jihar Kaduna bisa irin wannan karamci da suka nuna, wanda a cewarsa hakan na nuni da dorewar kyakkyawar alaka tsakanin NAF da jihar Kaduna, tun a shekarun 1960.

Ya kara da cewa, dama jihar Kaduna, ta kasance gida ce ga babban base na NAF da ma’aikatan da ke bakin aiki da wadanda suka yi ritaya.

Da yake karin haske kan dalilin da ya sa rundunar NAF ke ba da fifiko wajen samar da Gidaje masu sauki ga ma’aikatanta da suka yi ritaya, Air Marshall Abubakar ya ce: “ Babban abun alfaharin NAF shi ne jajirtattun ma’aikatanta, in babu kwarin guiwa ga ma’aikata, duk nagartar makami ba zai yi tasiri ba.” Ya ba da tabbacin cewa, za a yi amfani da filin ta yadda ya dace.

Filin da aka ware mai fadin hekta 43.746 shi ne na farko cikin biyu da Gwamna Sani ya amince a mika wa sojojin NAF. Filin na biyu mai fadin hekta 44.894 za a sake mikawa NAF bayan kammala duk matakan da suka dace kamar yadda Hukumar Babban Birnin Kaduna (KCTA) ta bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaNAFSojojin saman Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fetur Da Ake Amfani Da Shi Kullum A Nijeriya Ya Ragu Zuwa Lita Miliyan 44.3 –NMDPRA

Next Post

Wang Yi: Akwai Bukatar Mayar Da Dangantakar Sin Da Amurka Bisa Tafarki Mai Aminci Da Dorewa

Related

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe
Labarai

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

28 minutes ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

2 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

3 hours ago
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

11 hours ago
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi
Labarai

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

12 hours ago
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo
Labarai

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

12 hours ago
Next Post
Wang yi

Wang Yi: Akwai Bukatar Mayar Da Dangantakar Sin Da Amurka Bisa Tafarki Mai Aminci Da Dorewa

LABARAI MASU NASABA

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.