ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Mallaka Wa Rundujar Sojin Sama Fili Sama Da Hekta 43 Don Gina Gidaje

by Sulaiman
3 years ago
Uba sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Mai Girma Sanata Uba Sani a ranar 25 ga Oktoba, 2023 ya mika wa Shugaban Rundunar Sojin Sama (CAS), Air Marshal Hasan Abubakar takardun mallakar fili mai fadin hekta 43.746 da Jihar Kaduna ta ware wa Rundunar Sojojin Saman Nijeriya (NAF).

A sanarwar da Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Kaduna, Muhammad Lawal Shehu ya fitar, ta ce, an tanadi Filayen ne don gina jerin gidaje da manyan jami’an Rundunar NAF zasu amfana bayan sun ajiye aiki.

  • An Dawo Da Zirga-zirgar Jiragen Sama A Filin Jirgin Sama Na Kaduna
  • Gwamnati Ta Samo Jarin Fiye Da Dala Biliyan 2 A Bangaren Wutar Lantarki

Samuel Aruwan, Shugaban Hukumar Babban Birnin Kaduna (KCTA) wanda ya wakilci Gwamna Sani a wajen taron mika takardar filin a hedikwatar NAF da ke Abuja, ya mika takardun filin ne ga shugaban sojin rundunar sama ta Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Gwamna Sani ya yabawa CAS bisa jagorancin sa da kuma rundunar NAF bisa kokari da sadaukarwa wajen ci gaba da yaki da ta’addanci da ‘yan fashin daji da masu garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka a jihar Kaduna da ma kasa baki daya.

Aruwan, wanda kuma shi ne mai kula da ma’aikatar tsaron cikin gida da harkokin cikin gida, ya tabbatar wa NAF kudirin gwamnatin jihar wajen inganta jin dadin ma’aikatan NAF da ma jami’an tsaro baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

 

A nasa jawabin, CAS Hassan Abubakar ya yabawa Gwamna Sani da mutanen jihar Kaduna bisa irin wannan karamci da suka nuna, wanda a cewarsa hakan na nuni da dorewar kyakkyawar alaka tsakanin NAF da jihar Kaduna, tun a shekarun 1960.

Ya kara da cewa, dama jihar Kaduna, ta kasance gida ce ga babban base na NAF da ma’aikatan da ke bakin aiki da wadanda suka yi ritaya.

Da yake karin haske kan dalilin da ya sa rundunar NAF ke ba da fifiko wajen samar da Gidaje masu sauki ga ma’aikatanta da suka yi ritaya, Air Marshall Abubakar ya ce: “ Babban abun alfaharin NAF shi ne jajirtattun ma’aikatanta, in babu kwarin guiwa ga ma’aikata, duk nagartar makami ba zai yi tasiri ba.” Ya ba da tabbacin cewa, za a yi amfani da filin ta yadda ya dace.

Filin da aka ware mai fadin hekta 43.746 shi ne na farko cikin biyu da Gwamna Sani ya amince a mika wa sojojin NAF. Filin na biyu mai fadin hekta 44.894 za a sake mikawa NAF bayan kammala duk matakan da suka dace kamar yadda Hukumar Babban Birnin Kaduna (KCTA) ta bayyana.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
Wang yi

Wang Yi: Akwai Bukatar Mayar Da Dangantakar Sin Da Amurka Bisa Tafarki Mai Aminci Da Dorewa

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.