• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Jami’an Najeriya Na Amincewa Da Alfanun Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ga Kasashen Afrika

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Manyan Jami’an Najeriya Na Amincewa Da Alfanun Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ga Kasashen Afrika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bana ake cika shekaru 10 da gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, kuma a farkon watan Oktoba, na ziyarci Najeriya, wadda take daya daga wasu kasashen Afrika wadanda suka riga sauran kasashen duniya amincewar shawarar. Domin fahimtar amfanin shawarar ga kasar, na zanta da kakakin majalisar wakilai, da ministan harkokin wajen kasar.

Kakakin majalisar wakilan Najeriya Abbas Tajudeen ya ce, “Tashar teku ta Lekki da kamfanin CHEC ya gina, da layukan dogo, da sauran ayyukan da kamfanin CCECC ya gudanar, da ma yankin ciniki maras shinge na Lekki, da na Ougun da Guangdong da sauransu, ba ma kawai sun samar da dimbin guraben aikin yi ba ne, har ma sun ingiza bunkasuwar tattalin arziki ga al’ummar wurin.” Shawarar na amfanar al’ummar Najeriya matuka, kuma kasarsa za ta ci gaba da goyon bayan shawarar, a cewar Abbas Tajudeen.

  • Kamfanonin Sadarwa Na Kenya Sun Yi Hadin Gwiwa Da Na Sin Don Kaddamar Da Kamfanin Hada Wayoyin Hannu
  • An Kammala Taron Tsaro Na Xiangshan Karo Na 10 Na Beijing

A nasa bangare kuwa, ministan harkokin wajen kasar Yusufu Tuggar cewa ya yi, “A matsayin kasa mai yawan jama’a kuma mafi karfin tattalin arziki a Afrika, shawarar ta dace da tsarin raya kasa. Kaza lika kasashen biyu suna hadin kai a fannin samar da manyan ababen more rayuwa, da horar da kwrarru, da dai sauran bangarori, ciki hadda tashar Lekki, da jirgin kasa dake Lagos, da layin dogon dake tsakanin Abuja da Kaduna, wanda ya kasance irinsa na farko a Afrika dake amfani da fasaha da ma’aunin Sin, da kuma sabon filin saukar jiragen sama na Abuja, wanda ya zama sabuwar alamar Abuja.

Ban da wannan kuma, na dawo nan kasar Sin a tsakiyar watan Oktoba, inda na zanta da mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima, wanda ya halarci taron kolin kasa da kasa na tattaunawar hadin kai bisa shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na 3 a birnin Beijing, inda Shettima ya ce, shawarar na da babbar ma’ana ga bunkasuwar Afrika, wadda ta taka mihimmiyar rawa wajen samar da manyan ababen more rayuwa a kasashen. Alal misali a Najeriya, layukan dogo da kasashen biyu suka yi hadin kai wajen ginawa na da amfani matuka ga kafa tsarin zirga-zirga a kasar, da raya tattalin arziki da kyautata zaman rayuwar jama’a. Layin dogon tsakanin Abuja da Kaduna da aka riga ake amfani da shi na ingiza bunkasuwar tattalin arziki da al’ummar Najeriya sosai. Ban da wannan kuma, Shettima ya ce, yayin zantawarsa da shugaban Sin Xi Jinping, sun kai ga matsaya daya, kan hadin kai a bangaren manyan ababen more rayuwa, kuma za a ci gaba da sa kaimi ga shimfida layukan dogo da dai sauran ayyuka a Najeriya.

Manyan jami’an Najeriya da dama suna amincewa da damammaki, da bunkasuwa da shawarar take kawowa kasashen Afirka, musamman ma Najeriya. A ganinsu, shawarar na taka rawa wajen raya manyan ababen more rayuwa, da kyautata zaman rayuwar jama’a, da daga karfin takarar kasarsu, har ma da samar da makoma mai haske a fannin hadin kai da cin moriya tare a nan gaba.

Labarai Masu Nasaba

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

Ci gaban da Najeirya ke samu bayan ta shiga wannan shawara, ta zama misali ga amfanin shawarar ga Afrika har ma ga dukkanin fadin duniya. An yi imanin cewa, a cikin shekaru 10 masu zuwa, karin kasashe musamman ma kasashen Afrika, za su amince da wannan shawara da za su shiga, don more damammakin shawarar, da kuma kara amincewa tsakanin Sin da kasashen Afrika a bangaren siyasa, da al’adu, da hadin kan tattalin arziki, har ma ta kai ga taka rawa wajen samun zaman lafiya da karko a duniya baki daya. (Mai rubuta: Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Nasarar Harba Tauraron Dan Adam Na Tianhui-5 

Next Post

An Mai Da Hankali Kan Ci Gaba Mai Inganci Yayin Taron Koli Kan Harkokin Kudi Na Sin

Related

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

51 minutes ago
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021
Daga Birnin Sin

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

2 hours ago
Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

3 hours ago
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

23 hours ago
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

24 hours ago
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5
Daga Birnin Sin

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

1 day ago
Next Post
Sin

An Mai Da Hankali Kan Ci Gaba Mai Inganci Yayin Taron Koli Kan Harkokin Kudi Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

July 28, 2025
Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

July 28, 2025
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

July 28, 2025
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

July 28, 2025
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

July 28, 2025
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

July 28, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.