ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Jami’an Najeriya Na Amincewa Da Alfanun Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ga Kasashen Afrika

by CGTN Hausa
3 years ago
Afrika

A bana ake cika shekaru 10 da gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, kuma a farkon watan Oktoba, na ziyarci Najeriya, wadda take daya daga wasu kasashen Afrika wadanda suka riga sauran kasashen duniya amincewar shawarar. Domin fahimtar amfanin shawarar ga kasar, na zanta da kakakin majalisar wakilai, da ministan harkokin wajen kasar.

Kakakin majalisar wakilan Najeriya Abbas Tajudeen ya ce, “Tashar teku ta Lekki da kamfanin CHEC ya gina, da layukan dogo, da sauran ayyukan da kamfanin CCECC ya gudanar, da ma yankin ciniki maras shinge na Lekki, da na Ougun da Guangdong da sauransu, ba ma kawai sun samar da dimbin guraben aikin yi ba ne, har ma sun ingiza bunkasuwar tattalin arziki ga al’ummar wurin.” Shawarar na amfanar al’ummar Najeriya matuka, kuma kasarsa za ta ci gaba da goyon bayan shawarar, a cewar Abbas Tajudeen.

  • Kamfanonin Sadarwa Na Kenya Sun Yi Hadin Gwiwa Da Na Sin Don Kaddamar Da Kamfanin Hada Wayoyin Hannu
  • An Kammala Taron Tsaro Na Xiangshan Karo Na 10 Na Beijing

A nasa bangare kuwa, ministan harkokin wajen kasar Yusufu Tuggar cewa ya yi, “A matsayin kasa mai yawan jama’a kuma mafi karfin tattalin arziki a Afrika, shawarar ta dace da tsarin raya kasa. Kaza lika kasashen biyu suna hadin kai a fannin samar da manyan ababen more rayuwa, da horar da kwrarru, da dai sauran bangarori, ciki hadda tashar Lekki, da jirgin kasa dake Lagos, da layin dogon dake tsakanin Abuja da Kaduna, wanda ya kasance irinsa na farko a Afrika dake amfani da fasaha da ma’aunin Sin, da kuma sabon filin saukar jiragen sama na Abuja, wanda ya zama sabuwar alamar Abuja.

ADVERTISEMENT

Ban da wannan kuma, na dawo nan kasar Sin a tsakiyar watan Oktoba, inda na zanta da mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima, wanda ya halarci taron kolin kasa da kasa na tattaunawar hadin kai bisa shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na 3 a birnin Beijing, inda Shettima ya ce, shawarar na da babbar ma’ana ga bunkasuwar Afrika, wadda ta taka mihimmiyar rawa wajen samar da manyan ababen more rayuwa a kasashen. Alal misali a Najeriya, layukan dogo da kasashen biyu suka yi hadin kai wajen ginawa na da amfani matuka ga kafa tsarin zirga-zirga a kasar, da raya tattalin arziki da kyautata zaman rayuwar jama’a. Layin dogon tsakanin Abuja da Kaduna da aka riga ake amfani da shi na ingiza bunkasuwar tattalin arziki da al’ummar Najeriya sosai. Ban da wannan kuma, Shettima ya ce, yayin zantawarsa da shugaban Sin Xi Jinping, sun kai ga matsaya daya, kan hadin kai a bangaren manyan ababen more rayuwa, kuma za a ci gaba da sa kaimi ga shimfida layukan dogo da dai sauran ayyuka a Najeriya.

Manyan jami’an Najeriya da dama suna amincewa da damammaki, da bunkasuwa da shawarar take kawowa kasashen Afirka, musamman ma Najeriya. A ganinsu, shawarar na taka rawa wajen raya manyan ababen more rayuwa, da kyautata zaman rayuwar jama’a, da daga karfin takarar kasarsu, har ma da samar da makoma mai haske a fannin hadin kai da cin moriya tare a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Ci gaban da Najeirya ke samu bayan ta shiga wannan shawara, ta zama misali ga amfanin shawarar ga Afrika har ma ga dukkanin fadin duniya. An yi imanin cewa, a cikin shekaru 10 masu zuwa, karin kasashe musamman ma kasashen Afrika, za su amince da wannan shawara da za su shiga, don more damammakin shawarar, da kuma kara amincewa tsakanin Sin da kasashen Afrika a bangaren siyasa, da al’adu, da hadin kan tattalin arziki, har ma ta kai ga taka rawa wajen samun zaman lafiya da karko a duniya baki daya. (Mai rubuta: Amina Xu)

Afrika
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Sin

An Mai Da Hankali Kan Ci Gaba Mai Inganci Yayin Taron Koli Kan Harkokin Kudi Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.