• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Jami’an Najeriya Sun Amince Da Ci Gaban Hadin Kai Karkashin Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Manyan Jami’an Najeriya Sun Amince Da Ci Gaban Hadin Kai Karkashin Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu kasashen yamma sun dade suna karawa batun bashin da Sin take baiwa Afrika gishiri, musamman ma bayan an gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, sun bayyana bashin da Sin take baiwa kasashen Afirka a matsayin abin da zai haifar da matsalar bashi.

Irin wannan kalamai na cewa wai bashin da Sin take baiwa Afrika tarko ne, na da nufin hana bunkasuwar hadin kan Sin da Afirka da cin moriya tare.

  • Xi Ya Gana Da Firaministan Girka Da Yin Tattaunawa Da Shugaban Gwamnatin Jamus
  • Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

Sinawa na da wani karin magana dake nuna cewa, idan ana son tabbatar da ganin bunkasuwar tattalin arziki, dole ne a fara ne da gina hanyoyi. Shi ya sa, rancen kudin da Sin take baiwa Najeriya wajen aiwatar da ayyukan hadin gwiwa karkashin wannan shawara ta “ziri daya da hanya daya”, yawancinsu ana amfani da su wajen samar da manyan ababen more rayuwa. Alal misali, an gina layin dogo na farko mai amfani da ma’aunin Sin a Afrika, wato layin dogo dake tsakanin Abuja da Kaduna a Najeirya, da kuma layin dogo na farko dake cikin birni a yammacin Afirka, wato layin dogo na Abuja na Najeirya.

A can baya tsohon shugaban kasar Nijeriya Muhammadu Buhari ya taba shaidawa manema labarai cewa, rancen kudin da Sin take baiwa Najeriya, an yi amfani da su ne wajen gina layin dogo, da hanyoyin mota da dai sauransu, kuma idan babu irin wadannan ayyuka, al’ummar kasar ba yadda za su yi sai su yi zirga-ziraga da kafafu. Ya kuma yi maraba da duk wata kasa dake iya baiwa kasarsa taimako a fannin gina manyan ababen mora rayuwa.

Amma shin me ya hana wadannan kasashen yamma?

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

A farkon watan bara na kai ziyara a Najeriya, na kuma zanta da kakakin majalisar wakilan tarayyar Nijeriya Abbas Tajudeen, kuma yayin zantawar mu ya ce, kasashe da dama suna shirin baiwa Najeriya rancen kudi, amma kasashen Afrika suna zabar rancen da ya dace da yanayin da suke ciki. Idan an kwatanta da manufofin sauran kasashe, rancen kudin da Sin ta samar na kunshe da kudin ruwa mai araha, da wa’adi mai tsawo. Najeriya na godiya sosai kan taimakon da Sin take ba ta wajen raya tattalin arzikinta. Ban da wannan, bisa rahotannin da wasu hukumomin kasa da kasa, da kungiyoyin nazari suka bayar, an ce, yawancin basusukan da kasashen Afirka suke karba na fitowa ne daga daidaikun mutane na kasashen yamma.

Kasashen Afrika na da ma’ auninsu na zabar abokan hadin gwiwa, bisa la’akari da moriyarsu. A halin yanzu, karin kasashe sun karbi shawarar “ziri daya da hanya daya”. Alkawarin da gwamnatin kasar Sin ta dauka game da hadin gwiwar shawarar daddade ne, kuma ya dace da muradunsu, shi ya sa ta samu amincewa daga kasashe, da jama’arsu da suka karbi shawarar. Ban da wannan kuma, rancen kudin da Sin take baiwa kasashen, ana amfani da su ne wajen gina manyan ababen more rayuwa, matakin da zai ingiza bunkasuwar tattalin arzikinsu. Kaza lika idan an yi hangen nesa, za a ga cewa zai taimakawa wadannan kasashe wajen biyan bashin da kasashen yamma, da wasu hukumomin kudaden kasa da kasa suke binsu. (Mai zana da rubuta: MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CIIEKamfanin CCECC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Baje Kolin CIIE Zai Ja Hankalin Manyan Kasuwancin Da Ake Yi Ta Na’urorin Zamani

Next Post

Yadda Uwargida Za Ta Hada Boga

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

15 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

16 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

17 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

18 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

20 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

2 days ago
Next Post
Yadda Uwargida Za Ta Hada Boga

Yadda Uwargida Za Ta Hada Boga

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.