ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Jami’an Najeriya Sun Amince Da Ci Gaban Hadin Kai Karkashin Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

by CGTN Hausa
3 years ago
Najeriya

Wasu kasashen yamma sun dade suna karawa batun bashin da Sin take baiwa Afrika gishiri, musamman ma bayan an gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, sun bayyana bashin da Sin take baiwa kasashen Afirka a matsayin abin da zai haifar da matsalar bashi.

Irin wannan kalamai na cewa wai bashin da Sin take baiwa Afrika tarko ne, na da nufin hana bunkasuwar hadin kan Sin da Afirka da cin moriya tare.

  • Xi Ya Gana Da Firaministan Girka Da Yin Tattaunawa Da Shugaban Gwamnatin Jamus
  • Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

Sinawa na da wani karin magana dake nuna cewa, idan ana son tabbatar da ganin bunkasuwar tattalin arziki, dole ne a fara ne da gina hanyoyi. Shi ya sa, rancen kudin da Sin take baiwa Najeriya wajen aiwatar da ayyukan hadin gwiwa karkashin wannan shawara ta “ziri daya da hanya daya”, yawancinsu ana amfani da su wajen samar da manyan ababen more rayuwa. Alal misali, an gina layin dogo na farko mai amfani da ma’aunin Sin a Afrika, wato layin dogo dake tsakanin Abuja da Kaduna a Najeirya, da kuma layin dogo na farko dake cikin birni a yammacin Afirka, wato layin dogo na Abuja na Najeirya.

ADVERTISEMENT

A can baya tsohon shugaban kasar Nijeriya Muhammadu Buhari ya taba shaidawa manema labarai cewa, rancen kudin da Sin take baiwa Najeriya, an yi amfani da su ne wajen gina layin dogo, da hanyoyin mota da dai sauransu, kuma idan babu irin wadannan ayyuka, al’ummar kasar ba yadda za su yi sai su yi zirga-ziraga da kafafu. Ya kuma yi maraba da duk wata kasa dake iya baiwa kasarsa taimako a fannin gina manyan ababen mora rayuwa.

Amma shin me ya hana wadannan kasashen yamma?

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

A farkon watan bara na kai ziyara a Najeriya, na kuma zanta da kakakin majalisar wakilan tarayyar Nijeriya Abbas Tajudeen, kuma yayin zantawar mu ya ce, kasashe da dama suna shirin baiwa Najeriya rancen kudi, amma kasashen Afrika suna zabar rancen da ya dace da yanayin da suke ciki. Idan an kwatanta da manufofin sauran kasashe, rancen kudin da Sin ta samar na kunshe da kudin ruwa mai araha, da wa’adi mai tsawo. Najeriya na godiya sosai kan taimakon da Sin take ba ta wajen raya tattalin arzikinta. Ban da wannan, bisa rahotannin da wasu hukumomin kasa da kasa, da kungiyoyin nazari suka bayar, an ce, yawancin basusukan da kasashen Afirka suke karba na fitowa ne daga daidaikun mutane na kasashen yamma.

Kasashen Afrika na da ma’ auninsu na zabar abokan hadin gwiwa, bisa la’akari da moriyarsu. A halin yanzu, karin kasashe sun karbi shawarar “ziri daya da hanya daya”. Alkawarin da gwamnatin kasar Sin ta dauka game da hadin gwiwar shawarar daddade ne, kuma ya dace da muradunsu, shi ya sa ta samu amincewa daga kasashe, da jama’arsu da suka karbi shawarar. Ban da wannan kuma, rancen kudin da Sin take baiwa kasashen, ana amfani da su ne wajen gina manyan ababen more rayuwa, matakin da zai ingiza bunkasuwar tattalin arzikinsu. Kaza lika idan an yi hangen nesa, za a ga cewa zai taimakawa wadannan kasashe wajen biyan bashin da kasashen yamma, da wasu hukumomin kudaden kasa da kasa suke binsu. (Mai zana da rubuta: MINA)

Najeriya
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Yadda Uwargida Za Ta Hada Boga

Yadda Uwargida Za Ta Hada Boga

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.