• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Wayar Da Kan Malamai Game Da Ajiyar Kudin Aikin Hajjin 2024 A Kaduna

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
An Wayar Da Kan Malamai Game Da Ajiyar Kudin Aikin Hajjin 2024 A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna, ta yi kira ga malaman addinin Musulunci da su taimaka wajen wayar da kan duk wasu maniyyata aikin Hajji kan bukatar gaggauta biyan kudaden ajiya don cika wa’adin ranar 31 ga Disamba, 2023.

Babban sakataren hukumar, Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu, ya bayyana cewa hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta tsayar da wa’adin watan Disamba a matsayin ranar karshe na rijistar maniyyata aikin hajjin 2024.

  • An Kwace Kambun Hilda Baci A Gasar Dafa Abinci Ta Duniya
  • Neja Na Neman Kaso 13 Na Kudaden Lantarki Da Ake Samu Daga Ruwa A Yankinta

Dokta Arigasiyyu ya yi wannan roko ne a yayin wani taron wayar da kan al’umma da aka shirya wa limamai da malamai daga gundumomi yankin 23 da aka gudanar a kananan hukumomin Kaduna da Sabon Gari a jiya.

A cewarsa, za a aike da kudin aikin Hajjin maniyyatan zuwa NAHCON a ranar 31 ga watan Disamba, 2023, domin bai wa hukumar damar shirin aikin Hajjin badi yadda ya dace.

Dokta Alrigasiyyu ya ce ma’anar wannan tsari shi ne shigar da dukkan limaman masallatan Juma’a na jihar domin su ne masu ruwa da tsaki a harkokin Hajji.

Labarai Masu Nasaba

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sakataren zartarwa ya yi nuni da cewa limamai sun fi kusanci da maniyyata, don haka akwai bukatar a musu bayani game da wa’adin da aka ware don jan hankalin jama’a.

Ya ce bisa sabbin ka’idojin, bayar da biza zai fara ne watanni biyu kafin gudanar da aikin Hajji, sakamakom sauyi da kasar Saudiyya ta yi a kalandar tsarin aikin hajji.

Dokta Arigasiyyu ya bayyana cewa saboda wannan sauyi ya sa ake bukatar dukkan maniyyata su yi biya kudinsu kafin karshen wa’adin watan Disamba.

A nasa jawabin mukaddashin shugaban ayyuka na hukumar, Alhaji Abubakar Yusuf ya ce hukumar za ta ci gaba da hada kai da malamai wajen wayar da kan dukkan maniyyatan game da sabbin tsare-tsare da NAHCON da na Saudiyya suka bullo da su na sauya fasalin aikin Hajji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin Hajjin 2024KadunaManiyyataNAHCON
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kwace Kambun Hilda Baci A Gasar Dafa Abinci Ta Duniya

Next Post

Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Yajin Aikin Da Za Mu Shiga – NLC

Related

Ministan Tsaro
Labarai

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

2 minutes ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

31 minutes ago
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya
Labarai

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

2 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

3 hours ago
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

12 hours ago
Next Post
Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Yajin Aikin Da Za Mu Shiga - NLC

LABARAI MASU NASABA

Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.