ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Wayar Da Kan Malamai Game Da Ajiyar Kudin Aikin Hajjin 2024 A Kaduna

by Sadiq
2 years ago
Aikin Hajji

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna, ta yi kira ga malaman addinin Musulunci da su taimaka wajen wayar da kan duk wasu maniyyata aikin Hajji kan bukatar gaggauta biyan kudaden ajiya don cika wa’adin ranar 31 ga Disamba, 2023.

Babban sakataren hukumar, Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu, ya bayyana cewa hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta tsayar da wa’adin watan Disamba a matsayin ranar karshe na rijistar maniyyata aikin hajjin 2024.

  • An Kwace Kambun Hilda Baci A Gasar Dafa Abinci Ta Duniya
  • Neja Na Neman Kaso 13 Na Kudaden Lantarki Da Ake Samu Daga Ruwa A Yankinta

Dokta Arigasiyyu ya yi wannan roko ne a yayin wani taron wayar da kan al’umma da aka shirya wa limamai da malamai daga gundumomi yankin 23 da aka gudanar a kananan hukumomin Kaduna da Sabon Gari a jiya.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, za a aike da kudin aikin Hajjin maniyyatan zuwa NAHCON a ranar 31 ga watan Disamba, 2023, domin bai wa hukumar damar shirin aikin Hajjin badi yadda ya dace.

Dokta Alrigasiyyu ya ce ma’anar wannan tsari shi ne shigar da dukkan limaman masallatan Juma’a na jihar domin su ne masu ruwa da tsaki a harkokin Hajji.

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

Sakataren zartarwa ya yi nuni da cewa limamai sun fi kusanci da maniyyata, don haka akwai bukatar a musu bayani game da wa’adin da aka ware don jan hankalin jama’a.

Ya ce bisa sabbin ka’idojin, bayar da biza zai fara ne watanni biyu kafin gudanar da aikin Hajji, sakamakom sauyi da kasar Saudiyya ta yi a kalandar tsarin aikin hajji.

Dokta Arigasiyyu ya bayyana cewa saboda wannan sauyi ya sa ake bukatar dukkan maniyyata su yi biya kudinsu kafin karshen wa’adin watan Disamba.

A nasa jawabin mukaddashin shugaban ayyuka na hukumar, Alhaji Abubakar Yusuf ya ce hukumar za ta ci gaba da hada kai da malamai wajen wayar da kan dukkan maniyyatan game da sabbin tsare-tsare da NAHCON da na Saudiyya suka bullo da su na sauya fasalin aikin Hajji.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026
Labarai

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
Labarai

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Next Post
Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Yajin Aikin Da Za Mu Shiga - NLC

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.