ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Wayar Da Kan Malamai Game Da Ajiyar Kudin Aikin Hajjin 2024 A Kaduna

by Sadiq
3 years ago
Aikin Hajji

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna, ta yi kira ga malaman addinin Musulunci da su taimaka wajen wayar da kan duk wasu maniyyata aikin Hajji kan bukatar gaggauta biyan kudaden ajiya don cika wa’adin ranar 31 ga Disamba, 2023.

Babban sakataren hukumar, Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu, ya bayyana cewa hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta tsayar da wa’adin watan Disamba a matsayin ranar karshe na rijistar maniyyata aikin hajjin 2024.

  • An Kwace Kambun Hilda Baci A Gasar Dafa Abinci Ta Duniya
  • Neja Na Neman Kaso 13 Na Kudaden Lantarki Da Ake Samu Daga Ruwa A Yankinta

Dokta Arigasiyyu ya yi wannan roko ne a yayin wani taron wayar da kan al’umma da aka shirya wa limamai da malamai daga gundumomi yankin 23 da aka gudanar a kananan hukumomin Kaduna da Sabon Gari a jiya.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, za a aike da kudin aikin Hajjin maniyyatan zuwa NAHCON a ranar 31 ga watan Disamba, 2023, domin bai wa hukumar damar shirin aikin Hajjin badi yadda ya dace.

Dokta Alrigasiyyu ya ce ma’anar wannan tsari shi ne shigar da dukkan limaman masallatan Juma’a na jihar domin su ne masu ruwa da tsaki a harkokin Hajji.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Sakataren zartarwa ya yi nuni da cewa limamai sun fi kusanci da maniyyata, don haka akwai bukatar a musu bayani game da wa’adin da aka ware don jan hankalin jama’a.

Ya ce bisa sabbin ka’idojin, bayar da biza zai fara ne watanni biyu kafin gudanar da aikin Hajji, sakamakom sauyi da kasar Saudiyya ta yi a kalandar tsarin aikin hajji.

Dokta Arigasiyyu ya bayyana cewa saboda wannan sauyi ya sa ake bukatar dukkan maniyyata su yi biya kudinsu kafin karshen wa’adin watan Disamba.

A nasa jawabin mukaddashin shugaban ayyuka na hukumar, Alhaji Abubakar Yusuf ya ce hukumar za ta ci gaba da hada kai da malamai wajen wayar da kan dukkan maniyyatan game da sabbin tsare-tsare da NAHCON da na Saudiyya suka bullo da su na sauya fasalin aikin Hajji.

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Yajin Aikin Da Za Mu Shiga - NLC

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.