• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamishinan Cinikayya Da Zuba Jari Na Najeriya Dake Shanghai Ya Yaba Da Manufofin Kasar Sin Na Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kwamishinan Cinikayya Da Zuba Jari Na Najeriya Dake Shanghai Ya Yaba Da Manufofin Kasar Sin Na Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bikin baje-kolin kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin karo na shida wato CIIE a birnin Shanghai dake gabashin kasar Sin, inda kwamishinan kula da harkokin cinikayya da zuba jari na yankin Asiya daga karamin ofishin jakadancin tarayyar Najeriya dake Shanghai, Ibrahim A. Ahmed ya yaba matuka da manufofin kasar Sin na fadada bude kofa ga kasashen waje, da kara shigo da kayayyaki daga kasashe daban-daban.

Wakilinmu Murtala Zhang dauke da karin bayani daga Shanghai.

  • Wakar Kidaya: Aisha Humaira Ta Nemi Al’umma Su Daina Tsangwamar Mawaki Rarara
  • Dandalin Hongqiao Na Maida Hankali Ga Kiyaye Tsarin Cinikayyar Sassa Daban Daban

Malam Ibrahim Ahmed ya ce, Najeriya na farin-cikin samun damar halartar bikin CIIE a wannan karo, ganin yadda yake samar da muhimmiyar dama ga tallata kayayyakin kasar, musamman amfanin gona da albarkatun kasa, inda ya ce:

“Tun fara bikin na bana, mutane da yawa sun zo nan don tambayar kayayyakinmu har sun yi odar wasu da dama. Mutane suna sha’awar kayayyakin Najeriya, wadanda suka bambanta da na sauran kasashen Afirka sosai. Kayayyakin Najeriya na da inganci sosai, kuma ina matukar farin-cikin ganin cewa suna samun karbuwa a wajen mutanen China.”

Sin

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Jami’in ya kara da cewa, kasar Sin ba ta taba barin kasashen Afirka a baya ba wajen samar da ci gaba, ganin yadda bikin CIIE din ke samar da wata muhimmiyar dama ga kasashen Afirka wajen raya harkokin kasuwanci, inda ya ce:

“Ya samar mana da damar mu’amala da masu zuba jari na kasar Sin, al’amarin dake da muhimmanci ga ci gaban tattalin arzikin Najeriya. Don haka muna godiya ga gwamnatin kasar Sin saboda damar da ta samar mana wajen tallata kayayyakinmu a wannan bikin.”

Malam Ibrahim Ahmed ya yi karin haske cewa, Najeriya ta cimma nasarori da dama wajen halartar bikin CIIE tun daga irinsa na farko da aka yi a shekara ta 2018, kuma a bana, yana son tallata wasu muhimman nau’o’in amfanin gona, musamman gyada, da ridi, da busasshiyar citta, da sauran wasu albarkatun ma’adinai.

Sin

Da ya tabo batun burin da Najeriya take son cimmawa a wajen bikin CIIE na bana, jami’in ya ce:

“Muna fatan ganin kamfanoni da ’yan kasuwanmu kanana da matsakaita sun samu damar tallata kayayyakinsu da kyau, don kara samun ci gaban sana’o’insu.” (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaTattalin Arzikin sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Kada Kuri’a: CIIE Na Kara Kuzari Kan Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Ganawar Shugabannin Sin Da Australia Ta Share Fagen Kyautata Dangantaka

Related

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

19 hours ago
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

20 hours ago
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

21 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

22 hours ago
Sin
Daga Birnin Sin

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

23 hours ago
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000
Daga Birnin Sin

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

1 day ago
Next Post
Ganawar Shugabannin Sin Da Australia Ta Share Fagen Kyautata Dangantaka

Ganawar Shugabannin Sin Da Australia Ta Share Fagen Kyautata Dangantaka

LABARAI MASU NASABA

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

September 9, 2025
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

September 9, 2025
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

September 9, 2025
Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

September 9, 2025
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

September 9, 2025
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

September 9, 2025
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

September 9, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.