ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar Shugabannin Sin Da Australia Ta Share Fagen Kyautata Dangantaka

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da firaministan Australia Anthony Albanese wanda ya yi ziyarar aiki a Sin. Yayin zantawar shugabannin 2 a ranar Litinin a birnin Beijing, Xi ya jaddada bukatar hadin gwiwar sassan biyu, ta yadda za su gina kyakkyawar alaka bisa daidaito, da cimma matsaya, da kawar da sabani, da hadin gwiwar cimma moriya tsakaninsu. 

A nasa tsokacin kuwa, firaminista Albanese ya ce Australia da Sin na da banbanci ta fuskar tsarin siyasa, kuma hakan ba wata matsala ba ce, sai dai bai dace a bari sabanin ya gurgunta yanayin dangantakar sassan biyu ba. Ya ce tattaunawa da hadin gwiwa ne zabin da ya dace Australia da Sin su runguma.

  • Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Kasa Da Kasa Na Wuzhen Kan Intanet
  • Darajar Cinikayyar Kasar Sin A Ketare Ya Karu Da Kaso 0.03% Cikin Watanni 10 Na Bana

Wannan ne dai karon farko da wani firaministan Australia ya ziyarci kasar Sin cikin shekaru 7 da suka gabata. Kaza lika alakar Sin da Australia na cikin muhimman manufofin kasar Sin game da kasashen yamma masu ci gaba. A matsayinta na babbar abokiyar huldar cinikayyar Australia, sauye-sauye, da bude kofa, da zamanantarwa da Sin ke aiwatarwa na ingiza samuwar damammaki masu tarin yawa ga Australia.

ADVERTISEMENT

To sai dai kuma duk da haka, a zamanin gwamnatocin Australia biyu da suka gabata, kasar ta rungumi manufar nan ta Amurka mai lakabin “Indo-Pacific strategy”, wadda a karkashinta aka hana karbar fasahar 5G ta kamfanin Huawei, kana aka rika takalar kasar Sin ta fakewa da batutuwa kamar na jihar Xinjiang da tekun kudancin Sin, wanda hakan ya kai ga haifar da koma baya ga dangantakar dake tsakanin Sin da Australia, tare da illata moriyar Australia.

A watan Nuwanban shekarar bara ne kuma, a tsibirin Bali na kasar Indonesiya, shugaba Xi ya gana da mista Albanese wanda jim kadan da kama aikin firaministan kasar Australiya, ya kuma share fagen farfadowa, da kuma inganta alakar Sin da kasarsa. Yayin ganawarsu ta wannan karo a birnin Beijing kuma, bangaren Sin ya jaddada bukatar lura matuka, da nuna adawa da manufofin dake yunkurin jefa yankin Asiya da Pacific cikin rudani, kana ya nuna dalilin da ya sa alakar Sin da Australia ta shiga mawuyacin hali a ’yan shekarun baya.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Alakar Sin da Australia, wadda ta ci karo da koma baya, a yanzu tana farfadowa cikin kuzari. Kaza lika ana fatan Sin da Australia za su rungumi yanayin zamanin da ake ciki, su kyautata fahimtar juna, da amincewar juna ta hanyar zaman jituwa, kana su cimma bunkasuwar bai daya ta hanyar hadin gwiwar cimma moriya tare. (Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Next Post
Manzon Musamman Na Sin Kan Batun Yankin Gabas Ta Tsakiya Zai Halarci Taron Tallafin Jin Kai A Gaza

Manzon Musamman Na Sin Kan Batun Yankin Gabas Ta Tsakiya Zai Halarci Taron Tallafin Jin Kai A Gaza

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.