• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

byCGTN Hausa
2 years ago
Sin

Tun bayan barkewar sabon zagayen tashin hankali tsakanin Falasdinawa da dakarun Isra’ila, mutane sama da 11,000 sun rasa rayukansu a Gaza, wanda hakan ya yi matukar tada hankalin sassan kasa da kasa, kuma tuni kasashen duniya suka fara kiraye-kirayen ganin an gaggauta dakatar da bude wuta, tare da kawo karshen zubar da jini.

A bangaren sassa dake taka rawar gani wajen ganin an kawo karshen wannan tashin hankali, ko shakka babu kasar Sin ta yi fice, ganin yadda tun farkon lamarin mahukuntan take ta tattaunawa da sassan masu ruwa da tsaki, kaza lika Sin ta yi tsayin daka wajen tattaunawa da ragowar kasashen duniya karkashin kwamitin tsaron MDD, kana ta yi duk mai yiwuwa wajen ingiza dawo da zaman lafiya, da kai zuciya nesa, domin ganin an yayyafawa wutar tashin hankalin ruwa.

  • Sin Na Da Mutane Sama Da Miliyan 364 Dake Amfani Da Hidimomin Kiwon Lafiya Ta Yanar Gizo
  • Taron MDD: Gwamntin Tarayya Za Ta Dauki Nauyin Gudanar Da Makarantar UNESCO A Nijeriya – Minista

Bisa himma da kasar Sin ke yi, da mayar da hankali sosai kan wannan lamari, ta lura da manyan bukatun da ake da su na shawo kan lamarin, har ma ta gabatar da matsaya karkashin jigo 4.

Da farko dai kasar Sin na tsaye kan burin tabbatar da an kare mutuntaka, wato aiwatar da dukkanin matakai na kare hakkokin dan Adam na rayuwa, kamar dai yadda dokokin jin kai na kasa da kasa suka tanada. Na biyu kuwa, Sin ta yi amanar cewa, aiwatar da matakan siyasa ne kadai za su ba da damar kawo karshen yakin da ake gwabzawa tsakanin Falasdinawa da tsagin Isra’ila. Sai kuma na uku, wato cudanyar sassa daban daban, ta fannin shawarwari da aiwatar da matakan da suka dace, wanda zai taimaka matuka wajen ganin bayan wannan rikici. Sannan kuma na hudu, Sin ta yi imanin cewa, wajibi ne a magance tushe, da kuma abubuwan da suka haifar da wannan rikici wanda ke ta maimaituwa tsawon lokaci. Karkashin hakan, kasar Sin na ganin dole ne a tabbatar da kafuwar kasashe biyu masu cin gashin kansu, matakin da zai tabbatar da cikakken ’yancin Falasdinawa na samun kasarsu.

Idan mun yi la’akari na wadannan batutuwa da Sin ke tsaye a kansu, tabbas za mu gamsu da kyakkyawar manufar kasar, ta ganin an kawo karshen zubar jini tsakanin wadannan sassa biyu, da ma cimma burin ganin an bunkasa zaman lafiya da jituwa a gabas ta tsakiya.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Bankin Jama’ar Sin: Fasahar Kudin Sin Na Sahun Gaba A Duniya

Bankin Jama'ar Sin: Fasahar Kudin Sin Na Sahun Gaba A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version