ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Tun bayan barkewar sabon zagayen tashin hankali tsakanin Falasdinawa da dakarun Isra’ila, mutane sama da 11,000 sun rasa rayukansu a Gaza, wanda hakan ya yi matukar tada hankalin sassan kasa da kasa, kuma tuni kasashen duniya suka fara kiraye-kirayen ganin an gaggauta dakatar da bude wuta, tare da kawo karshen zubar da jini.

A bangaren sassa dake taka rawar gani wajen ganin an kawo karshen wannan tashin hankali, ko shakka babu kasar Sin ta yi fice, ganin yadda tun farkon lamarin mahukuntan take ta tattaunawa da sassan masu ruwa da tsaki, kaza lika Sin ta yi tsayin daka wajen tattaunawa da ragowar kasashen duniya karkashin kwamitin tsaron MDD, kana ta yi duk mai yiwuwa wajen ingiza dawo da zaman lafiya, da kai zuciya nesa, domin ganin an yayyafawa wutar tashin hankalin ruwa.

  • Sin Na Da Mutane Sama Da Miliyan 364 Dake Amfani Da Hidimomin Kiwon Lafiya Ta Yanar Gizo
  • Taron MDD: Gwamntin Tarayya Za Ta Dauki Nauyin Gudanar Da Makarantar UNESCO A Nijeriya – Minista

Bisa himma da kasar Sin ke yi, da mayar da hankali sosai kan wannan lamari, ta lura da manyan bukatun da ake da su na shawo kan lamarin, har ma ta gabatar da matsaya karkashin jigo 4.

ADVERTISEMENT

Da farko dai kasar Sin na tsaye kan burin tabbatar da an kare mutuntaka, wato aiwatar da dukkanin matakai na kare hakkokin dan Adam na rayuwa, kamar dai yadda dokokin jin kai na kasa da kasa suka tanada. Na biyu kuwa, Sin ta yi amanar cewa, aiwatar da matakan siyasa ne kadai za su ba da damar kawo karshen yakin da ake gwabzawa tsakanin Falasdinawa da tsagin Isra’ila. Sai kuma na uku, wato cudanyar sassa daban daban, ta fannin shawarwari da aiwatar da matakan da suka dace, wanda zai taimaka matuka wajen ganin bayan wannan rikici. Sannan kuma na hudu, Sin ta yi imanin cewa, wajibi ne a magance tushe, da kuma abubuwan da suka haifar da wannan rikici wanda ke ta maimaituwa tsawon lokaci. Karkashin hakan, kasar Sin na ganin dole ne a tabbatar da kafuwar kasashe biyu masu cin gashin kansu, matakin da zai tabbatar da cikakken ’yancin Falasdinawa na samun kasarsu.

Idan mun yi la’akari na wadannan batutuwa da Sin ke tsaye a kansu, tabbas za mu gamsu da kyakkyawar manufar kasar, ta ganin an kawo karshen zubar jini tsakanin wadannan sassa biyu, da ma cimma burin ganin an bunkasa zaman lafiya da jituwa a gabas ta tsakiya.

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

MASU ALAKA

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya
Daga Birnin Sin

Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

June 27, 2026
Next Post
Bankin Jama’ar Sin: Fasahar Kudin Sin Na Sahun Gaba A Duniya

Bankin Jama'ar Sin: Fasahar Kudin Sin Na Sahun Gaba A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.