ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Tun bayan barkewar sabon zagayen tashin hankali tsakanin Falasdinawa da dakarun Isra’ila, mutane sama da 11,000 sun rasa rayukansu a Gaza, wanda hakan ya yi matukar tada hankalin sassan kasa da kasa, kuma tuni kasashen duniya suka fara kiraye-kirayen ganin an gaggauta dakatar da bude wuta, tare da kawo karshen zubar da jini.

A bangaren sassa dake taka rawar gani wajen ganin an kawo karshen wannan tashin hankali, ko shakka babu kasar Sin ta yi fice, ganin yadda tun farkon lamarin mahukuntan take ta tattaunawa da sassan masu ruwa da tsaki, kaza lika Sin ta yi tsayin daka wajen tattaunawa da ragowar kasashen duniya karkashin kwamitin tsaron MDD, kana ta yi duk mai yiwuwa wajen ingiza dawo da zaman lafiya, da kai zuciya nesa, domin ganin an yayyafawa wutar tashin hankalin ruwa.

  • Sin Na Da Mutane Sama Da Miliyan 364 Dake Amfani Da Hidimomin Kiwon Lafiya Ta Yanar Gizo
  • Taron MDD: Gwamntin Tarayya Za Ta Dauki Nauyin Gudanar Da Makarantar UNESCO A Nijeriya – Minista

Bisa himma da kasar Sin ke yi, da mayar da hankali sosai kan wannan lamari, ta lura da manyan bukatun da ake da su na shawo kan lamarin, har ma ta gabatar da matsaya karkashin jigo 4.

ADVERTISEMENT

Da farko dai kasar Sin na tsaye kan burin tabbatar da an kare mutuntaka, wato aiwatar da dukkanin matakai na kare hakkokin dan Adam na rayuwa, kamar dai yadda dokokin jin kai na kasa da kasa suka tanada. Na biyu kuwa, Sin ta yi amanar cewa, aiwatar da matakan siyasa ne kadai za su ba da damar kawo karshen yakin da ake gwabzawa tsakanin Falasdinawa da tsagin Isra’ila. Sai kuma na uku, wato cudanyar sassa daban daban, ta fannin shawarwari da aiwatar da matakan da suka dace, wanda zai taimaka matuka wajen ganin bayan wannan rikici. Sannan kuma na hudu, Sin ta yi imanin cewa, wajibi ne a magance tushe, da kuma abubuwan da suka haifar da wannan rikici wanda ke ta maimaituwa tsawon lokaci. Karkashin hakan, kasar Sin na ganin dole ne a tabbatar da kafuwar kasashe biyu masu cin gashin kansu, matakin da zai tabbatar da cikakken ’yancin Falasdinawa na samun kasarsu.

Idan mun yi la’akari na wadannan batutuwa da Sin ke tsaye a kansu, tabbas za mu gamsu da kyakkyawar manufar kasar, ta ganin an kawo karshen zubar jini tsakanin wadannan sassa biyu, da ma cimma burin ganin an bunkasa zaman lafiya da jituwa a gabas ta tsakiya.

LABARAI MASU NASABA

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

MASU ALAKA

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
Daga Birnin Sin

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Next Post
Bankin Jama’ar Sin: Fasahar Kudin Sin Na Sahun Gaba A Duniya

Bankin Jama'ar Sin: Fasahar Kudin Sin Na Sahun Gaba A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.