• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan ‘Yan Takarar Da Za Su Fafata A Zaben Gwamnan Jihar Kogi

by Sadiq
2 years ago
Kogi

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta shirya tsaf domin gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi da Imo da kuma Bayelsa.

Za a gudanar da zabukan jihohin ne a ranar Asabar, 11 ga watan Nuwamban 2023.

  • Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani
  • Gwamnonin PDP Sun Karyata Shirin Mubaya’a Ga Tinubu

A tsawon watanni bakwai da suka wuce, ‘yan takarar gwamna a jihar Kogi, na ta gudanar da yakin neman zabe a kokarin su na ganin sun kai ga nasara.

Yanzu haka akwai ‘yan takara 18 da ke takarar gwamnan a jihar ta Kogi.

‘Yan takarar za su fafata ne domin ganin wanda zai maye gurbin gwamna Yahaya Bello mai barin gado, wanda ke kammala wa’adin mulkinsa karo na biyu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

Jam’iyyar APC mai mulkin jihar na yin duk mai yiwuwa wajen ganin ta rike kujerar gwamnan yayin da jam’iyyun adawa kuma ke kokarin ganin sun kwace mulki daga hannun APC da ke kan mulki tsawon shekaru takwas.

Cikin jam’iyyu 18 da INEC ta tantance domin shiga zaben gwamna a jihar Kogi ya zuwa ranar 9 ga watan Nuwamban, 2023, ana ganin cewa shida ne kawai ke a kan gaba gabanin zaben na ranar Asabar.

Masana harkokin siyasa a jihar na ganin cewa fafatawar za ta fi zafi ne tsakanin jam’iyyu uku; APC, PDP, da kuma SDP.

Masanan sun kara da cewa manyan ‘yan takarar uku da ke sahun gaba a zaben sun fito ne daga kabilu daban-daban, kamar Ebira, Igala, da kuma Okun, kuma hakan zai iya yin tasiri sosai kan sakamakon zaben.

Sun ce yayin da jam’iyyar APC za ta iya samun yawan kuri’u daga tsakiyar jihar, SDP kuma za ta iya bayar da mamaki a gabashin jihar, inda ita kuma PDP mai dimbin magoya baya a yammacin jihar, za su zabi Dino Melaye.

Manyan ‘yan takarar guda uku da za su fafatawa a tsakaninsu su ne:

Sanata Dino Melaye – PDP

Sanata Dino Melaye shi ne mutumin da zai yi wa jam’iyyar PDP takara a zaben gwamnan Kogi a yau Asabar.

An haife shi ne a watan Janairun 1974 kuma dan siyasa ne mai yawan haifar da cece-kuce.

Tsohon Sanatan, ya yi karatun sakandare a Kwalejin Abdulaziz Attah, da ke Okene.

Daga nan ya tafi Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya a shekarar 2000 inda ya karanta ilimin Geography.

A shekara ta 2021, ya kammala karatu a Jami’ar Baze, inda ya karanta fannin Shari’a.

Melaye ya wakilci mazabar Kogi ta Yamma a majalisar dattawa daga 2015-2019.

Zamansa dan takarar jam’iyyar PDP, ya kara iza wutar adawa tsakaninsa da jam’iyyar APC a jihar.

Ana kuma ganin cewa dimbin magoya bayan jam’iyyar PDP na tare da shi, kuma suna shirye domin zaben shi a matsayin gwamnan jihar Kogi.

Ododo Ahmed Usman – APC

Ododo Usman shi ne dan takarar zaben gwamnan jihar Kogi a karkashin jam’iyyar APC a zaben da za a yi.

Usman-Ododo wanda dan kabilar Ebira ne da ya fito daga garin Okene, ya yi digirinsa na farko a fannin Akanta a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.

Ya kuma yi digirinsa na biyu a fannin kasuwanci a Jami’ar Legas.

Kafin samun zama dan takarar gwamna a jam’iyyar APC, ya kasance babban mai binciken kudi na kananan hukumomin jihar, tsawon shekara bakwai da rabi, kuma an yi imanin cewa ya taka rawar gani a gwamnatin Yahaya Bello.

Murtala Yakubu Ajaka – SDP

Murtala Yakubu Ajaka ya kasance babban jigo a jam’iyyar APC a jihar Kogi, kafin komawarsa SDP.

Mista Ajaka ya fito ne daga karamar hukumar Igalamela, da ke gabashin jihar Kogi. Mazabar tana da yawan masu kada kuri’a.

Ya koma jam’iyyar SDP ne bayan kasa samun tikiti a APC, inda daga bisani ya samu nasarar zama dan takarar SDP a zaden gwamnan Kogi na 2023.

An yi imanin cewa dan takarar na SDP na iya samun kuri’u masu yawa a gabashin Kogi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Manyan Labarai

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Next Post
Filin Jirgin Tafawa

Bauchi Ta Mika Ragamar Filin Jirgin Tafawa Balewa Ga Tarayya

LABARAI MASU NASABA

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.