• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Ayyukan Naira Miliyan 873.66 A Jami’ar Tafawa Balewa

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Tafawa balewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da bayar da fifiko ga manyan makarantu, musamman domin a rinka yaye daliban da za su samu ilimin zamani mai inganci da zai yi daidai da na fadin duniya.

Tinubu ya sanar a hakan ne a yayin da yake yin jawabi a taron kaddamar da ayyuka shida da suka lashe sama da naira miliyan 873.66 a jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da na kwalejin kimiyya da fasaha ta Tatari Ali dukkan su da ke Jihar Bauchi.

  • Bauchi Ta Mika Ragamar Filin Jirgin Tafawa Balewa Ga Tarayya
  • Gwamnonin PDP Sun Karyata Shirin Mubaya’a Ga Tinubu

Gine-ginen da aka kaddamar sun kunshi tsangayar kimiyya da fasaha da kuma sashen tsangayar fasaha da ke a jami’ar ta Abubakar Tafawa Balewa, sai kuma na dakin taro da dakunan yin gwaje-gwajen magunguna a jami’ar Tatari Ali, wadanda aka gina su daga cikin kudin tallafi na asusun hukumar TETFund na shekarar 2021 zuwa shekarar 2022.

Tinubu wanda ministan kula da harkokin kasashen waje, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ya wakilce shi a gurin taron ya sanar da cewa, bunkasa fannin ilimin zamani na daya daga cikin ayyukan da gwamnatin tarayya a karkashin shugabancin jam’iyyar APC ta bai wa fifiko.

Shugaban ya kara da cewa, kirkiro da shirin bai wa daliban jama’a rancen kudin karatu da gwamnatin ta yi, ta yi don ta saukaka wa daliban wajen gudanar da karatunsu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Acewarsa, gwamnatin ta kuma gana da kungiyar dalibai ta manyan makaratu ta kasa (NANS) don tattaunawa a kan jin dadi da walwalar dailban.

Ya ce, wannan na daga cikin kokarin da gwamnatin ke kan ci gaba da yi don magance kalubalen da daliban manyan makartun kasar ke fuskatan da kuma samar da kyakyawan yanayi a tsakanin gwamnatin da kuma kungiyon daliban na manyan makaratun kasar nan.

Kazalika, Tinubu ya sanar da cewa, a kwanan baya gwamnatinsa ta dakatar da umarnin ba aikin yi ba biyan albashi da ta kakaba wa kungiyar malaman jami’o’in kasar nan (ASUU), wanda wannan umarnin, ya ba su damar karbar albashinsu da gwamnatin ta rike saboda yajin aikin da suka yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUATBUTETFund
ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Bukatar Gwamnati Ta Rika Bai Wa Kamfanonin Gida Aiki – Injiniya Isyaku

Next Post

Kano Ta Raba Tallafi Fiye Da Na Tarayya  – Musa Falaki

Related

Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

10 hours ago
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja
Labarai

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

11 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

12 hours ago
Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi
Manyan Labarai

Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi

16 hours ago
Zaman lafiya
Labarai

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

18 hours ago
Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri
Manyan Labarai

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

19 hours ago
Next Post
Gwamna Yusuf

Kano Ta Raba Tallafi Fiye Da Na Tarayya  - Musa Falaki

LABARAI MASU NASABA

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

May 29, 2025
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

May 29, 2025
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

May 29, 2025
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

May 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

May 29, 2025
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

May 29, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

May 29, 2025
AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

May 29, 2025
Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.