• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwa Ta Yi Shahada Bayan Karya Dan Bindiga Da Tabarya Wajen Kare Danta

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Uwa Ta Yi Shahada Bayan Karya Dan Bindiga Da Tabarya Wajen Kare Danta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tura dai ta fara kai al’umma bango dangane da irin cin kashin da ‘yan bindiga masu garguwa da mutane ke yi, inda wata uwa mai suna Maryam Muhammad ‘yar shekara 52 ta ceci rayuwar danta daga hannun masu garkuwa a kauyen Sabon Garin Jada da ke karamar hukumar Alkaleri a Jihar Bauchi.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, Malama Maryam ta gamu da ajalinta a lokacin da ta kare danta daga hannun masu garkuwa da mutane, inda ta yi kukan kura ta nufi kansu da tabarya har ma ta karya daya daga cikin masu garkuwan, lamarin da ya sanya suka bude mata wuta har ta rasu nan take.

  • Da Diminsa: ‘Yan Daba Sun Farmaki ‘Yan Majalisar Bauchi Tare Da Farfasa Motoci

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa, Marigayiya Maryam mai ‘ya’ya takwas a duniya ta nufi kan masu garkuwa da mutanen ne a lokacin da suka mamaye gidanta da ke sabon Garin Jada da nufin su yi garkuwa da danta ko illata shi, inda ta ce sam hakan ba zai yiyu ba.

Idan za ku iya tunawa dai, a ranar Alhamis da ta gabata ne dai wasu gungun ‘yan bindiga suka kashe mutum hudu tare da mutum uku a wani harin da suka kai yankin Alkaleri.

Wakilinmu ya zanta da diyar marigayiyar, Hauwa’u Muhammad ‘yar shekara 26, inda ta yi cikakken bayanin yadda lamari ya faru, ta ce, ‘yan bindigan sun so sace yayanta ne sai kuma mamarsu ta yi kokarin hana su har sai da ‘yan bindigan suka bude mata wuta.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

“Da daren ranar Litinin da misalin karfe 12 wasu mutane suka shigo cikin gidanmu tare da kokarin yin garkuwa da yayana. Ita kuma mahaifiyarmu ta taso domin ta taimaka masa, a wannan yanayin ne suka harbe har lahira, inda muke addu’a Allah ya mata rahama,” Hauwau ta shaida cikin kuka.

Ta kara da cewa yayan nata bai mutu ba, amma sun ji masa raunuka a kai. Ta ce ‘yan bindigan da suka shigo gidansu sun kai mutum 11.

Da yake nasa jawabin a wajen jajantawa kan rasuwar marigayiya a ranar Asabar da gabata, gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad Abdulkadir ya ayyana Marigayiya Maryam a matsayin wata jarumar da ta bar abin koyi ga al’umma, ya misalta cewa lokacin da za a ji tsoron ‘yan bindiga ya wuce.

A cewarsa, “Abun da ya faru a wannan garin a gaskiya ya zama abun jaje sosai a garemu. Mun rasa ‘yar uwa, muna fatan Allah ya amshi shahadarta.

Wannan mata ta zama abin koyi a garemu a matsayinta na uwa wacce ta nuna mana mata ma suna iya jajircewa, ba ta yi mutuwar banza ba, ta yi mutuwar shahada insha Allahu, Allah ya jikanta ya rahama.”

Gwamna Bala Muhammad ya daura da cewa, “Mun zo nan garin ne domin mu jajanta muku ga wannan lamari wanda ya zama ruwan dare a Nijeriya.

“A yadda ake ma Jihar Bauchi tana da tsaro, amma abun yana son ya addabemu, sai dai ba za mu kwanta muna barci ba, za mu yi iya bakin kokarinmu mu wajen rayukanku da dukiyarku, kuma ya kamata a sani tsaro abu ne da ya kasance hakki ne a kan kowa.”

Gwamnan ya roki sarakuna da malamai da jama’a da su kara ninka addu’o’i domin samun nasarar shawo kan matsalolin tsaro da suke addabar kasar nan. Ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da suke amsa kiran jama’a a kowani tare da hanzarin kawo dauki idan jama’a sun bukaci hakan, musamman a lokacin da suke cikin yanayi na neman agajin gaggawa.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Alkaleri, Yusuf Garba ya bayyana cewar suna samun matsalar tsaro a yankinsu ne sakamakon iyaka da suka yi da jihohin Bauchi da Taraba wanda aka kashe mutum hudu a garin, ya nemi hadin kan jama’a domin samun nasara.

Shi kuma kwamishinan ‘yansandan Jihar Bauchi, CP Umar Sanda ya roki jama’a ne da su samar musu da bayanan sirri da zai taimaka wa hukumomin tsaro a kowani lokaci wajen yaki da matsalar tsaro.

A ‘yan kwanakin baya dai an yi ta samu rahotonnin matsalolin tsaro a Jihar Bauchi don ko a kwanakin baya ma an yi garkuwa da Hakimin kauyen Zira da ke karamar hukumar Toro tare da dansa daga bisani aka sako su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasannin Cin Kofin Nahiyar Afirka Na Mata Sun Kankama

Next Post

Buhari Ya Kaddamar Da Hanyar Nguru-Gashua-Bayamari A Yobe

Related

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Labarai

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

2 hours ago
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 
Labarai

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

3 hours ago
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

3 hours ago
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Labarai

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

4 hours ago
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
Labarai

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

4 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

5 hours ago
Next Post
Buhari Ya Kaddamar Da Hanyar Nguru-Gashua-Bayamari A Yobe

Buhari Ya Kaddamar Da Hanyar Nguru-Gashua-Bayamari A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.