ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwa Ta Yi Shahada Bayan Karya Dan Bindiga Da Tabarya Wajen Kare Danta

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Shahada

Tura dai ta fara kai al’umma bango dangane da irin cin kashin da ‘yan bindiga masu garguwa da mutane ke yi, inda wata uwa mai suna Maryam Muhammad ‘yar shekara 52 ta ceci rayuwar danta daga hannun masu garkuwa a kauyen Sabon Garin Jada da ke karamar hukumar Alkaleri a Jihar Bauchi.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, Malama Maryam ta gamu da ajalinta a lokacin da ta kare danta daga hannun masu garkuwa da mutane, inda ta yi kukan kura ta nufi kansu da tabarya har ma ta karya daya daga cikin masu garkuwan, lamarin da ya sanya suka bude mata wuta har ta rasu nan take.

  • Da Diminsa: ‘Yan Daba Sun Farmaki ‘Yan Majalisar Bauchi Tare Da Farfasa Motoci

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa, Marigayiya Maryam mai ‘ya’ya takwas a duniya ta nufi kan masu garkuwa da mutanen ne a lokacin da suka mamaye gidanta da ke sabon Garin Jada da nufin su yi garkuwa da danta ko illata shi, inda ta ce sam hakan ba zai yiyu ba.

ADVERTISEMENT

Idan za ku iya tunawa dai, a ranar Alhamis da ta gabata ne dai wasu gungun ‘yan bindiga suka kashe mutum hudu tare da mutum uku a wani harin da suka kai yankin Alkaleri.

Wakilinmu ya zanta da diyar marigayiyar, Hauwa’u Muhammad ‘yar shekara 26, inda ta yi cikakken bayanin yadda lamari ya faru, ta ce, ‘yan bindigan sun so sace yayanta ne sai kuma mamarsu ta yi kokarin hana su har sai da ‘yan bindigan suka bude mata wuta.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Da daren ranar Litinin da misalin karfe 12 wasu mutane suka shigo cikin gidanmu tare da kokarin yin garkuwa da yayana. Ita kuma mahaifiyarmu ta taso domin ta taimaka masa, a wannan yanayin ne suka harbe har lahira, inda muke addu’a Allah ya mata rahama,” Hauwau ta shaida cikin kuka.

Ta kara da cewa yayan nata bai mutu ba, amma sun ji masa raunuka a kai. Ta ce ‘yan bindigan da suka shigo gidansu sun kai mutum 11.

Da yake nasa jawabin a wajen jajantawa kan rasuwar marigayiya a ranar Asabar da gabata, gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad Abdulkadir ya ayyana Marigayiya Maryam a matsayin wata jarumar da ta bar abin koyi ga al’umma, ya misalta cewa lokacin da za a ji tsoron ‘yan bindiga ya wuce.

A cewarsa, “Abun da ya faru a wannan garin a gaskiya ya zama abun jaje sosai a garemu. Mun rasa ‘yar uwa, muna fatan Allah ya amshi shahadarta.

Wannan mata ta zama abin koyi a garemu a matsayinta na uwa wacce ta nuna mana mata ma suna iya jajircewa, ba ta yi mutuwar banza ba, ta yi mutuwar shahada insha Allahu, Allah ya jikanta ya rahama.”

Gwamna Bala Muhammad ya daura da cewa, “Mun zo nan garin ne domin mu jajanta muku ga wannan lamari wanda ya zama ruwan dare a Nijeriya.

“A yadda ake ma Jihar Bauchi tana da tsaro, amma abun yana son ya addabemu, sai dai ba za mu kwanta muna barci ba, za mu yi iya bakin kokarinmu mu wajen rayukanku da dukiyarku, kuma ya kamata a sani tsaro abu ne da ya kasance hakki ne a kan kowa.”

Gwamnan ya roki sarakuna da malamai da jama’a da su kara ninka addu’o’i domin samun nasarar shawo kan matsalolin tsaro da suke addabar kasar nan. Ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da suke amsa kiran jama’a a kowani tare da hanzarin kawo dauki idan jama’a sun bukaci hakan, musamman a lokacin da suke cikin yanayi na neman agajin gaggawa.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Alkaleri, Yusuf Garba ya bayyana cewar suna samun matsalar tsaro a yankinsu ne sakamakon iyaka da suka yi da jihohin Bauchi da Taraba wanda aka kashe mutum hudu a garin, ya nemi hadin kan jama’a domin samun nasara.

Shi kuma kwamishinan ‘yansandan Jihar Bauchi, CP Umar Sanda ya roki jama’a ne da su samar musu da bayanan sirri da zai taimaka wa hukumomin tsaro a kowani lokaci wajen yaki da matsalar tsaro.

A ‘yan kwanakin baya dai an yi ta samu rahotonnin matsalolin tsaro a Jihar Bauchi don ko a kwanakin baya ma an yi garkuwa da Hakimin kauyen Zira da ke karamar hukumar Toro tare da dansa daga bisani aka sako su.

Shahada
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Buhari Ya Kaddamar Da Hanyar Nguru-Gashua-Bayamari A Yobe

Buhari Ya Kaddamar Da Hanyar Nguru-Gashua-Bayamari A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.