• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Mulkin mallaka

Mulkin mallaka wata hanya ce ta tafiyar da gwamnati inda Turawan Ingila suka yi amfani da Sarakunan gargajiya wajen tafiyar da harkokin mulkinsu a yammacin Afirka. Shugaban ko jagoran al’amarin mulkin mallaka a yammacin Afirka shi ne Lord Frederick Lugard a shekarar1906.Ya fara gwada tafiyar da tsarin mulkin ne a Arewacin Nijeriya lokacin da aka ga abin an samu nasara,sai aka fara amfani da shi a sauran sassan kasashen yammacin Afirka.

An amince da Sarakunan gargajiya
Sarakuna wadanda sune ke lura da al’amuran da suka shafi al’umma a Arewacin Nijeriya al’umma suka nada su,don haka aka amince da sub a tare da wata matsala ba.Sune suka jagoranci hukumomin da ake tafiyar da al’amuran da suka shafi al’umma da ake kiran su da suna Natibe Authority. Shi ya sa babu wata matsala idan Sarakuna suka bayar da umarnin daya zo daga wurin jami’an Turawa na yin wani abu,hakan ta kasance ne saboda al’umma sun saba da samun umarni na wani abu daga wurin Sarakunan.

Sarakunan gargajiya ba su wasa da ba da umarni
Lokacin da gwamna Lord Lugard ya aiwatar da mulkin mallaka na Turawan Ingila a Arewacin Nijeriya,tun kafin lokacin da akwai hanyar da ake tafiyar da sarautar gargajiya ta tafiyar da al’umma.Sarakunan ko Sultan tuni akwai wuraren da suke karkashinsu suna mulkarsu ba tare da matsala ba,mutane kuma sun saba da al’amarin. Shi yasa mulkin ba a samu wata matsalar tafiyar da shi ba wanda yake da alaka da siyasa.

Al’amarin Haraji
Al’ummar Arewacin Nijeriya sun saba da al’amarin daya shafi Haraji saboda kuwa Talakawa sun saba da biyan Haraji nau’oi daban daban da suka hada da Jangali na dabbobi da wadanda mutane suke biya,shi yasa ba a samu wata matsala ba domin al’ummar Arewa sun saba da biyan su nau’oin harajin,domin an samu yin gyara ne lokacin da aka bullo da shi lokacin da aka fara tafiyar da mulkin mallaka a Arewacin Nijeriya.

Rashin Masu Ilmin Zamani A Arewa
A Arewacin Nijeriya bamasu ilimin zamani a lokacin kamar yadda ake da su a Kudancin Nijeriya,saboda a lokacin a Arewacin Nijeriya akwai lauyoyi wadanda suka samu horo a Ingila da kuma ‘yan jarida,alal misali a Arewacin Nijeriya ba irin wadancan mutanen wadanda Turawan mulkin mallaka za su samu matsalar tunkararsu,ba kamar a Kudancin Nijeriya ba.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

Kotunan shariar musulunci
Mulkin mallaka na turawan Ingila ya samu nasara ne a Arewacin Nijeriya saboda dam tuni ana da tsarin shari’a karamar hukumar gargajiya da ake kira Natibe Authority a lokacin.Sarakuna a Arewacin Nijeriya suna da kotu inda ake shari’ar wadanda suka aikata laifi idan kuma aka samu mutum da aikata laifi ana iya yanke ma shi hukunci, wannan tsarin ne Lord Lugard ya amince da shi da yi ma shi gyara.Misali kotunan musulunci ba za su zartar da hukunci kisa ba, ba tare da amincewar jami’an Turawan mulkin mallaka da suke zaune a Larduna daban- daban a Nijeriya.

Umarnin Jami’an Ingila
Kasancewar jami’an Turawan Ingila a Arewacin Nijeriya inda suke kulawa da Larduna ana kiransu da sunan Rasdan sune suke ba Sarakunan gargajiya shawarwari, wanda hakan ne ya basu dama ta samun nasara a tafiyar da mulkinsu a Arewacin Nijeriya.Kwamishinonin Larduna su suka rika ba Sarakunan gargajiya a Arewa shawarar da ta tabbatar da mulkin Turawan Ingila ya samu nasara a yammacin Afirka.daudawa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
majalisar kasa
Tarihi

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

August 30, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Next Post
Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

October 16, 2025
An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.