• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Nasir Ya Gabatar Da Kasafin Kudin Naira Biliyan 250 Ga Majalisar Dokokin Kebbi

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Nasir Ya Gabatar Da Kasafin Kudin Naira Biliyan 250 Ga Majalisar Dokokin Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Nasir Idris na Jihar Kebbi, ya gabatar da kasafin kudi naira biliyan 250, 134, 091, 757.01 na shekarar 2024 na samar da ababen more rayuwa da kuma ayyukkan ciyar da al’ummar jihar a gaban majalisar dokoki don damar amincewa da kasafin kudin.

Dakta Nasir ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a zauren majalisar da ke Birnin Kebbi.

  • Bunkasuwar Sin Na Taka Rawa Ga Farfadowar Yankin Asiya Da Pacific
  • BRICS Ta Bi Sahun Sassan Dake Neman Kawo Karshen Rikicin Isra’ila Da Palasdinu

Kasafin kudin samar da ababen more rayuwa da karfafa wa al’ummar jihar da kuma biyan bukatun ‘yan jihar da kuma cika alkawuran da aka dauka a yayin yakin neman zabe da aka yi wa jama’armu.

Gwamnan, ya ce a yayin gabatar da kasafin kudin na shekarar 2024 da za a kashe kudaden da ake kashewa akai-akai na biliyan 90.6, yayin da manyan kudaden da za a kashe ya kai biliyan 159.4.

Wasu muhimman sassa na tattalin arzikin jihar sun samu karin kasafin kudi saboda matakin da gwamnati ta dauka na samar da sabon shirin jihar Kebbi.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Ya ce wani bangare na shirin shi ne “magance batutuwan da suka hada da samar da ayyukan yi ga matasa da mata, gyara makarantu, gina hanyoyi, tsaro da samar da ingantaccen ruwan sha da kalubalen muhalli a jihar.

“A karkashin kasafin kudin 2024, nan take za mu kara habaka manufofinmu da aka tsara da kuma dorewar shirinmu a jihar”.

Dokta Nasir ya ce shirin gwamnatin na samar da ababen more rayuwa zai yi nisa wajen samar da hanyoyin samar da ababen more rayuwa da inganta rayuwar al’ummar jihar ta Kebbi kai tsaye, wanda hakan zai shafi al’ummar Jihar Kebbi kai tsaye, inda ya kara da cewa irin wannan shirin zai shafi gyaran makarantu da gina tituna da kuma zamanantar da jihar.

“Kudirin kasafin kudin shekarar 2024 na nuni da cewa an zuba jari mai yawa wajen samar da ingantaccen ruwan sha, da karfafawa mata da kungiyoyin matasa ta hanyar samar da ayyukkan yi.

Ya kuma ba da tabbacin ga ‘yan majalisar jihar na ci gaba da zaman lafiya da zamantakewar aiki.

Yayin da yake jinjina wa majalisar dokokin jihar kan kokarin da suke yi na nuna kyakykyawan sakamako doka ga daukacin al’ummar jihar.

A nasa martanin, kakakin majalisar dokokin jihar, Hon. Usman Muhammad ya bai wa gwamna Nasir Idris tabbacin yin gaggawar amincewa da kasafin kudin shekarar 2024 da aka gabatar wa majalisar domin amincewa.

Yayin da yake yi wa gwamnan alkawarin tabbataci da kasafin kudin da za a kashe zai biya bukatun ‘yan jihar domin ‘yan majalisar su ma wakilan jama’ar jihar ne daga mazabu daban-daban na jihar.

Daga karshe ya gode wa gwamna Nasir Idris bisa jajircewarsa ga ci gaban jihar da al’ummarta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasafin KudiKebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bunkasuwar Sin Na Taka Rawa Ga Farfadowar Yankin Asiya Da Pacific

Next Post

Lauyoyi Sun Bukaci Kotun ECOWAS Ta Haramta Takunkumi Kan Nijar

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

3 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

14 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

20 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

21 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da ÆŠansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

22 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da ÆŠansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

23 hours ago
Next Post
Lauyoyi Sun Bukaci Kotun ECOWAS Ta Haramta Takunkumi Kan Nijar

Lauyoyi Sun Bukaci Kotun ECOWAS Ta Haramta Takunkumi Kan Nijar

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.