ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Nasir Ya Gabatar Da Kasafin Kudin Naira Biliyan 250 Ga Majalisar Dokokin Kebbi

by Sadiq
3 years ago
Nasir

Gwamna Nasir Idris na Jihar Kebbi, ya gabatar da kasafin kudi naira biliyan 250, 134, 091, 757.01 na shekarar 2024 na samar da ababen more rayuwa da kuma ayyukkan ciyar da al’ummar jihar a gaban majalisar dokoki don damar amincewa da kasafin kudin.

Dakta Nasir ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a zauren majalisar da ke Birnin Kebbi.

  • Bunkasuwar Sin Na Taka Rawa Ga Farfadowar Yankin Asiya Da Pacific
  • BRICS Ta Bi Sahun Sassan Dake Neman Kawo Karshen Rikicin Isra’ila Da Palasdinu

Kasafin kudin samar da ababen more rayuwa da karfafa wa al’ummar jihar da kuma biyan bukatun ‘yan jihar da kuma cika alkawuran da aka dauka a yayin yakin neman zabe da aka yi wa jama’armu.

ADVERTISEMENT

Gwamnan, ya ce a yayin gabatar da kasafin kudin na shekarar 2024 da za a kashe kudaden da ake kashewa akai-akai na biliyan 90.6, yayin da manyan kudaden da za a kashe ya kai biliyan 159.4.

Wasu muhimman sassa na tattalin arzikin jihar sun samu karin kasafin kudi saboda matakin da gwamnati ta dauka na samar da sabon shirin jihar Kebbi.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ya ce wani bangare na shirin shi ne “magance batutuwan da suka hada da samar da ayyukan yi ga matasa da mata, gyara makarantu, gina hanyoyi, tsaro da samar da ingantaccen ruwan sha da kalubalen muhalli a jihar.

“A karkashin kasafin kudin 2024, nan take za mu kara habaka manufofinmu da aka tsara da kuma dorewar shirinmu a jihar”.

Dokta Nasir ya ce shirin gwamnatin na samar da ababen more rayuwa zai yi nisa wajen samar da hanyoyin samar da ababen more rayuwa da inganta rayuwar al’ummar jihar ta Kebbi kai tsaye, wanda hakan zai shafi al’ummar Jihar Kebbi kai tsaye, inda ya kara da cewa irin wannan shirin zai shafi gyaran makarantu da gina tituna da kuma zamanantar da jihar.

“Kudirin kasafin kudin shekarar 2024 na nuni da cewa an zuba jari mai yawa wajen samar da ingantaccen ruwan sha, da karfafawa mata da kungiyoyin matasa ta hanyar samar da ayyukkan yi.

Ya kuma ba da tabbacin ga ‘yan majalisar jihar na ci gaba da zaman lafiya da zamantakewar aiki.

Yayin da yake jinjina wa majalisar dokokin jihar kan kokarin da suke yi na nuna kyakykyawan sakamako doka ga daukacin al’ummar jihar.

A nasa martanin, kakakin majalisar dokokin jihar, Hon. Usman Muhammad ya bai wa gwamna Nasir Idris tabbacin yin gaggawar amincewa da kasafin kudin shekarar 2024 da aka gabatar wa majalisar domin amincewa.

Yayin da yake yi wa gwamnan alkawarin tabbataci da kasafin kudin da za a kashe zai biya bukatun ‘yan jihar domin ‘yan majalisar su ma wakilan jama’ar jihar ne daga mazabu daban-daban na jihar.

Daga karshe ya gode wa gwamna Nasir Idris bisa jajircewarsa ga ci gaban jihar da al’ummarta.

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Lauyoyi Sun Bukaci Kotun ECOWAS Ta Haramta Takunkumi Kan Nijar

Lauyoyi Sun Bukaci Kotun ECOWAS Ta Haramta Takunkumi Kan Nijar

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.