ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19

by Bashir Bello, Abuja
2 years ago
Dokoki

Sanata mai wakiltar Mazabar Borno ta Tsakiya, Sanata Kaka Shehu Lawan ya ga batar da wani kuduri na gaggawa da ke neman tattara dokokin da aka yi a kasar nan a tsakanin shekara 19. gaban zauren Majalisar Dattawa da ke Abuja.

Majalisar Dattawa ta umarci Kwamitocinta na Shari’a da na ‘Yancin Dan’adam da na Dokoki ba tare da bata lokaci ba su fara shiri domin tattara dokoki da aka yi a kasar nan daga shekara ta 2004 zuwa shekara ta 2023 a tarasu guri daya.

Sanatan ya ce dalilin sa na gabatar da wannan Kuduri shi ne ya lura cewa kimanin shekaru 19 kenan da aka tattara dokokin kasar nan wanda hakan ya haifar da rudani a kasa inda ake amfani da dokoki daban-daban masu karo da juna.

ADVERTISEMENT

Kaka ya kara da cewa ya lura cewa masu tallar littattafai a kan titunan suna dauke da kundin shari’a irin daban-daban a kasar nan; wanda hakan  koma baya ne ga kasar.

  • Kotun Daukaka Kara Ta Ce Tuntuben Alkalami Aka Samu Wajen Rubuta Kundin Hukuncin Shari’ar Zaben Kano

Ya kara da cewa, ya lura Malaman Makarantu a Jami’a da Dalibai kai har ma da Lauyoyi su ma suna amfani da Kundin Dokokin na Kasar nan iri daban-daban wanda hakan bai da ce ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Sanatan ya ci gaba da cewa, tun wancan lokaci zuwa yanzu Majalisar Tarayya ta yi dokoki masu tarin yawa wadanda shugabannin kasa daban-daban sun saka musu hannu amma har ya zuwa yanzu ba a tattara wadannan dokoki ba guri guda domin amfanar ‘Yan Nijeriya.

Sanatan wanda ya kara wa mane ma labarai haske a ofishinsa ya ce doka ce ta sahale wa ofishin Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya da ya gabatar da wannan bukata ta tattara dokokin na kasa tare da hadin gwiwa da Majalisar Tarayya.

Ya kara da cewa idan aka har-hada wadannan dokoki guri guda zai taimaka wajen gudanar da shari’a a Nijeriya ba tare da kawo rudani ba. In da ya ce a halin yanzu tabbas akwai rudani a yadda ake yanke hukunce-hukunce a Kotunan Nijeriya sakamakon bambance – bambance da ake samu a Kundin Shari’a.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna
Manyan Labarai

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Next Post
NNPP

NNPP Ta Bukaci Majalisar Shari’a Ta Kasa Ta Binciki Hukuncin Da Aka Yanke Wa  Gwamna Yusuf

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.