ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Sin

A halin yanzu a duk fadin kasar Sin, ana samun wani irin sabon sauyi kan abin da ya shafi kyautata walwalar rayuwar yau da kullum ta miliyoyin jama’a, inda gwamnatocin manyan birane ke bude hanyoyin kashe kudi da ciniki a bangaren gidajen cin abinci, da yawon bude ido, da wasannin motsa jiki da kuma harkokin nishadi.

 

Daga irin kamshin dake tashi a gidajen cin abinci na birnin Zhengzhou zuwa sowar masu sha’awar kwallon kwando a Zhejiang, za a fahimci irin yadda mahukuntan biranen suke bullo da shirye-shiryen bayar da tallafin kashe kudi domin kara kuzarin ruhin walwalar al’umma.

ADVERTISEMENT

 

A Guangzhou, ana bai wa masu sha’awar zuwa gidajen cin abinci wata kyakkyawar dama bisa yadda ake raba musu takardun tallafin cin abinci. A karkashin wannan tsari a zagaye na biyar, daga watan Disambar bara zuwa yanzu an raba takardun tallafin adadin yuan miliyan 100 wadda mutane suka yi amfani da su wajen ciye-ciye da tande-tande. Mahukuntan lardin Zhejiang sun fahimci yadda haduwar mutane a wuraren cin abinci ke inganta walwalarsu da kuma kara dankon soyayya da zumunci a tsakaninsu, kana da samar da karin karfi ga tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

 

Lardin Hubei shi ma ya bi sawu, inda ya bullo da nasa shirye-shiryen na raba takardun tallafin tare da mai da hankali musamman a kan bangaren da ya shafi cin abinci. Babban makasudin hakan shi ne a karfafa mutane su rika fita zuwa gidajen cin abinci. Wannan ya kara farfado da salon cin abinci tare a tsakanin Sinawa da kuma kwarya-kwaryan harkokin da ake yi a gefen wasu tituna bisa tsari. Baya ga bunkasa tattalin arziki, wannan dabara tana samar da yanayi mai dadi da faranta ran jama’a.

 

Shi ma birnin Shanghai ba a bar shi a baya ba a kan wannan sabga, inda shi kuma ya mayar da hankali a kan nishadantarwa ta fuskar al’adu. Birnin ya ware makudan kudi yuan miliyan 500 domin karfafa zuwan jama’a wurare da dandaloli na wasannin kwaiwakyo, da wasannin ban dariya, da harkokin wasanni na zamani da sauransu, inda a zagayen farko aka fara kashe yuan miliyan 30. A karkashin wannan tsarin na tallafi, mutane sun kashe fiye da yuan miliyan 91 a bangaren wasanni a birnin na Shanghai.

 

Shi kuwa lardin Zhejiang ya zo da wani salo ne na musamman mai hangen nesa, inda ya hade wasanni da yawon bude ido a bangaren karfafa walwalar jama’a da kashe kudi. Masu sha’awar kwallon kwando suna amfani da tikitin wasanni mai rangwame da lardin yake bayarwa don garzayawa wuraren wasanni masu jan hankali, da gidajen abinci da sauransu. Yin hakan wata fasaha ce ta karfafa hanyoyin taimakawa ci gaban tattalin arzikin cikin gida ta fuskar tsarin gudanar da rayuwar jama’a.

 

A can birnin Guangzhou ma, sama da mazauna birnin miliyan 6 ne suka yi amfani da takardun tallafin cin abinci, inda aka kashe yuan miliyan 409. Hakika wannan yana nuna cewa, duk lokacin da aka buda wa mutane sararin shiga a dama da su, to za su yi hakan da zuciya daya kuma cikin jin dadi.

 

A kwanan nan, wasu mahukunta a kasar Sin sun jaddada bukatar kara fadada hanyoyin cin gajiyar harkokin rayuwa na yau da kullum da ake kashe kudi wajen gudanar da su, don haka wadannan dabaru da gwamnatocin biranen suka bullo da su, suna ba su damar jifan tsuntsu biyu da dutse daya, ga amfanin da za a samu ta fuskar karuwar tattalin arziki musamman ga kananan masu sana’o’i, ga kuma inganta jin dadi da walwalar jama’a. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
  • Sulaiman
    An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

MASU ALAKA

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
Daga Birnin Sin

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
Daga Birnin Sin

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Next Post
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

LABARAI MASU NASABA

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.