ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Nijeriya Za Ta Mora Daga Taron Saudiyya Da Jamus

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Jamus

Masana na ci gaba da fashin baki kan taron kolin da aka gudanar ka bunkasa tattalin arziki a tsakanin Afirka da Saudiyya da kuma Jamus.

A makon jiya ne aka gudanar da na Saudiyya, yayin da na Jamus kuma ya gudana a wannan makon.

  • Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Bukace Lauyoyin Su Mayar Da Kwafin Takardun Shari’ar
  • Zaben Kano: ‘Yansanda Da Masu Zanga-zanga Sun Yi Arangama A Kano

LEADERSHIP Hausa ta tattauna da Kwamared Sabo Muhammad, wani mai sharhin lamuran yau da kullum da ke jihar Bauchi kan alfanun wannan taron, inda ya yi bayani kan taron Saudiyya.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, “Shugaba Bola Ahmed Tinubu irin wannan damar yake bukata domin jawo kasashe masu arziki kamar Saudiyya su zo su sanya hannun jari a musamman bangaren man fetur da iskar gas da sauransu. Na biyu kuma taron zai kara inganta kasuwanci da Saudiyya da sauran kasashen Labarawa. Abu na uku kuma shi ne domin ya tabbatar wa Saudiyya da sauran kasashe da suke da zimmar zuba jari, cewa yanzu ‘Njeriya’ wata kasa ce sabuwa wadda kofarta take a bude da ake kira ‘Free Market economy’ cewa za ka zo ka yi kasuwancinka cikin sauki kuma idan ka sanya hannun jarinka za ka samu riba mai inganci sannan babu wasu tarnake-tarnake da ake da su a baya, misali na idan ka sanya kudi babu wata wahala za ka fitar da kudinka kasar waje kamar yadda muka gani a baya. Manya-manyan kamfanoni na jiragen sama sun daina hulda da Nijeriya kamar British Airways da kuma kamfanonin da suke Daular Larabawa da kasashe da dama saboda ba su iya samun kudadensu na  waje da ake biya ta dalar Amurka.

“A wannan ziyarar na shugaban kasa ya tattauna da Yarima mai jiran gado Bin Salman har ma Saudiyya ta ke da zimmar cewa nan ba da jimawa ba za ta sanya kusan dalar Amurka miliyan dari biyar shi ne kimanin riyal din Saudiyya miliyan dubu biyu a matatun man fetur na Nijeriya wanda gwamnati take da su guda hudu kuma za su sanya hannun a kan yarjejeniyar yadda za a karfafa alakar na sauran fannoni da suka shafi makamashi ta yadda za a karfafa wa kan yadda ake tafiyar da harkokin makamashi na zamani kuma shi ministan tattalin arziki na kasar Saudiyya ya ce nan da karshen wannan shekarar ko a zangon farko na shekarar da za mu shiga za a zo a yi jarjejeniya a sanya hannu.”

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

A cewar masanin, Bola Tinubu na kokari ne don tabbatar wa kasashen da yake ziyarta cewa, gwamnatin Nijeriya a karkashinsa tana bi dukkanin dokoki na kasuwanci na kasa da kasa kamar misalign shawarar da ya bi ta cire tallafin mai da kudin da ake narkawa wajen kare darajar Naira.

“Sannan na uku kuma, tunin a kan haraji an riga an yi kwamiti mai karfi wanda zai cire dukkanin wata sarkakiya na na haraji daban-daban da suke sanya wa kamfanoni masu hannun jarida. Da kuma bukatar da shi shugaban kasa ya ke da ita cewa su yi aiki da kasashen duniya musamman ita Saudiyya da sauran kasashen duniya musamman na Labarawa domin a samu a yaki matsalar tsaro ta yadda shi shugaba Tinubu ke son Nijeriya da Saudiyya su yi aiki tare domin yaki da akidun kungiyoyi irin su Boko Haram, ISWAP da sauransu da ke Nijeriya da yankin Chadi.”

“Abu na uku idan suka yi aiki tare a bangaren tsaro akwai akwai yiwuwar ita kasar Saudiyya za ta fi bai wa Nijeriya taimako na kayan aiki da kuma na kudade da canza bayanai na sirri tun da akwai ISIS a Nijeriya kuma ISIS suna da karfi a kasashen Labarawa ka ga Nijeriya za ta samu bayanan sirri daga wajen  Saudiyya domin dakile kungiyon ISIS-ISWAP da sauran kungiyoyin ta’addanci, shi ya sanya ma a ziyarar akwai mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribado da shugaban tattara bayanai na sirri Malam Abbakar, to dukka wadannan alkairi ne, amma gaskiya ba za a ga wadannan alkairan a yanzu-yanzu ba.” Ya bayyana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Next Post
Masana Sun Yi Gargadi Kan Amfani Da Wani Sinadarin Gishiri A Nijeriya

Masana Sun Yi Gargadi Kan Amfani Da Wani Sinadarin Gishiri A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.