• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daure Matashi Shekara 2 Bisa Damfara Da Sunan Sojan Amurka

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
An Daure Matashi Shekara 2 Bisa Damfara Da Sunan Sojan Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Shiyyar Kaduna ta hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, ta tabbatar da samun hukuncin dauri ga wani Jesse Kassah, (mai suna Debaun Smith Wayne).

An yanke masa hukuncin daurin shekara biyu a gidan yari.

  • Shugaban Africa CDC Ya Yaba Da Hadin Gwiwar Sin Da Afrika A Bangaren Kiwon Lafiyar Al’umma
  • Za A Fuskanci Karancin Motoci A Nijeriya Sakamakon Karin Haraji

An samu Kassah da laifin yin kwaikwayon wani sojan Amurka kuma ya sayar da tikiti a Facebook ga wani Caitlin Morgan.

Kamar yadda bincike ya nuna, Kassah ya yi amfani da sunansa wajen damfarar wadanda abin ya shafa a cikin lamarin.

Mai shari’a Darius Khobo na babbar kotun Jihar Kaduna, Kaduna ne ya daure shi a gidan yari, bayan da ya amsa laifin da ake tuhumarsa da aikatawa a gaban kotu yayin da hukumar EFCC ta gurfanar da shi a gaban kuliya.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

An bayyana hakan ne ta hannun hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa a cikin wani sakon da ta wallafa a shafinta na D (tsohuwar Twitter).

Sanarwar ta kara da cewa, “Kai Jesse Joshua Kassah (aka Debaun Smith Wayne), (M) tsakanin watan Janairu zuwa Oktoba 2023 a Kaduna da ke karkashin ikon wannan kotun mai daraja, ka aikata laifi, kamar haka; karya ya gabatar da kanka a matsayin Debaun Smith Wayne; Wani jami’in sojan Amurka kuma mai sayar da tikiti a Facebook (wani shafin kafar yada labarun kan layi) ga wani Caitlin Morgan kuma wanda ya nuna cewa kun san karya ne sannan ka aikata laifin da ya saba wa doka kuma hukuncin da za a yi maka ya dace a karkashin sashe na 142 (1) na dokar Penal Code na Jihar Kaduna, na shekarar 2017″.

Ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi lokacin da aka karanta masa.

Da yake gabatar da rokonsa, lauyan masu shigar da kara, M. Arumemi, ya bukaci kotun da ta yanke wa wanda ake kara hukunci kamar haka.

Alkalin “ya yanke wa Kassah hukuncin daurin shekaru biyu a gidan yari tare da zabin tarar Naira 150,000.00.

Alkalin ya kuma bayar da umarnin a kwace wayar Samsung Galady A02 da aka yi amfani da ita wajen aikata laifin tare da mika ta ga Gwamnatin Tarayyar Nijeriya.

Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan shi ne karo na farko da Kassah zai tafi gidan gyaran hali a lokacin da aka kama shi a unguwar Karji da ke Kaduna bisa laifukan da suka shafi intanet.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Daure Wani Dan Kasuwa Bisa Laifin Satar Kayan Kanti

Next Post

Firimiyar Ingila: Man City Za Ta Karbi Bakuncin Liverpool A Etihad

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

4 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

4 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

4 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

1 month ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

1 month ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

1 month ago
Next Post
Firimiyar Ingila: Man City Za Ta Karbi Bakuncin Liverpool A Etihad

Firimiyar Ingila: Man City Za Ta Karbi Bakuncin Liverpool A Etihad

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.