ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
Tsaro

Tsoro ya haifar da rarrabuwar kawuna a kananan hukumomin Tureta da Dange/Shuni na Jihar Sokoto, yayin da hare-haren ‘yan bindiga ke ci gaba da addabar al’umma, lamarin da ya tilasta wa daruruwan iyalai tserewa daga gidajensu cikin halin kunci.

Tsawon watanni, mazauna yankin – musamman mata da yara – sun yi gudun hijira a cikin dare, suna neman mafaka a buɗaɗɗen wurare, dazuzzuka, da karkashin bishiyoyi, ba su iya kwana a cikin gida saboda ci gaba da barazanar tashin hankali.

  • Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu
  • Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

“Ban shiga gidana ba cikin wata uku,” in ji Halima, wata uwa mai ‘ya’ya hudu daga Tureta.

ADVERTISEMENT

“Kowane dare, muna kwana a karkashin bishiya, muna rayuwa cikin tsoro, tare da fargabar duk sautin da muka ii ‘yan fashi.”

Zanga-zanga a Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

A halin da ake ciki, mazauna kauyuka sama da 30 na gundumar Dan-Isa da Kagara a Karamar Hukumar Kaura-Namoda ta Jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana a Gusau babban birnin Jihar a ranar Alhamis.

Sun yi kira da gwamnati ta sa baki cikin gaggawa domin magance matsalar rashin tsaro da ke kara kamari a cikin al’ummominsu.

Masu zanga-zangar wadanda galibinsu mata da yara ne suka yi tattaki a kan titunan Gusau, rike da kwalaye masu dauke da saonni kamar haka: “Muna Bukatar Zaman Lafiya a Kauyukan Kaura-Namoda,” “Ya Kamata Gwamna Dauda Lawal da Matawalle Su Cece Mu,” “Ana Kashe Jama’ar Mu Kullum.

Da yake jawabi ga manema labarai a gaban gidan gwamnati da ke Gusau, daya daga cikin shugabannin al’ummar yankin, Lawal Kamilu daga Dan-Isa, ya bayyana zanga-zangar a matsayin kukan neman taimako bayan shafe shekaru ana kai hare-haren ‘yan fashi, da sace-sace da kashe-kashe.

“Mun fito ne daga kauyuka kusan 30. Mafi yawanmu a nan mata ne da kananan yara saboda yawancin mazajenmu ko dai an kashe su ko kuma ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su,” in ji Kamilu.

 

Martanin gwamnati

martanin da ya mayar, Kanar Ahmed Usman (mai ritaya), mai bai wa gwamnan Jihar Sokoto shawara kan harkokin tsaro, ya amince da zanga-zangar amma ya ce gwamnati na daukar matakan dawo da zaman lafiya.

“Jihar tana ci gaba da gudanar da ayyuka tare da hadin gwiwar jami’an tsaro, wanda aka samu gagarumar nasara,” in ji Kanar Usman.

“Saboda irin namijin kokarin da jami’an tsaronmu na yau da kullum da masu gadin al’umma suke yi, muna hada gwiwa da shugabannin al’umma domin dawo da zaman lafiya.

Tsaro
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.