ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daure Matashi Shekara 2 Bisa Damfara Da Sunan Sojan Amurka

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Damfara

Rundunar Shiyyar Kaduna ta hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, ta tabbatar da samun hukuncin dauri ga wani Jesse Kassah, (mai suna Debaun Smith Wayne).

An yanke masa hukuncin daurin shekara biyu a gidan yari.

  • Shugaban Africa CDC Ya Yaba Da Hadin Gwiwar Sin Da Afrika A Bangaren Kiwon Lafiyar Al’umma
  • Za A Fuskanci Karancin Motoci A Nijeriya Sakamakon Karin Haraji

An samu Kassah da laifin yin kwaikwayon wani sojan Amurka kuma ya sayar da tikiti a Facebook ga wani Caitlin Morgan.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda bincike ya nuna, Kassah ya yi amfani da sunansa wajen damfarar wadanda abin ya shafa a cikin lamarin.

Mai shari’a Darius Khobo na babbar kotun Jihar Kaduna, Kaduna ne ya daure shi a gidan yari, bayan da ya amsa laifin da ake tuhumarsa da aikatawa a gaban kotu yayin da hukumar EFCC ta gurfanar da shi a gaban kuliya.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

An bayyana hakan ne ta hannun hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa a cikin wani sakon da ta wallafa a shafinta na D (tsohuwar Twitter).

Sanarwar ta kara da cewa, “Kai Jesse Joshua Kassah (aka Debaun Smith Wayne), (M) tsakanin watan Janairu zuwa Oktoba 2023 a Kaduna da ke karkashin ikon wannan kotun mai daraja, ka aikata laifi, kamar haka; karya ya gabatar da kanka a matsayin Debaun Smith Wayne; Wani jami’in sojan Amurka kuma mai sayar da tikiti a Facebook (wani shafin kafar yada labarun kan layi) ga wani Caitlin Morgan kuma wanda ya nuna cewa kun san karya ne sannan ka aikata laifin da ya saba wa doka kuma hukuncin da za a yi maka ya dace a karkashin sashe na 142 (1) na dokar Penal Code na Jihar Kaduna, na shekarar 2017″.

Ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi lokacin da aka karanta masa.

Da yake gabatar da rokonsa, lauyan masu shigar da kara, M. Arumemi, ya bukaci kotun da ta yanke wa wanda ake kara hukunci kamar haka.

Alkalin “ya yanke wa Kassah hukuncin daurin shekaru biyu a gidan yari tare da zabin tarar Naira 150,000.00.

Alkalin ya kuma bayar da umarnin a kwace wayar Samsung Galady A02 da aka yi amfani da ita wajen aikata laifin tare da mika ta ga Gwamnatin Tarayyar Nijeriya.

Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan shi ne karo na farko da Kassah zai tafi gidan gyaran hali a lokacin da aka kama shi a unguwar Karji da ke Kaduna bisa laifukan da suka shafi intanet.”

Damfara
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Firimiyar Ingila: Man City Za Ta Karbi Bakuncin Liverpool A Etihad

Firimiyar Ingila: Man City Za Ta Karbi Bakuncin Liverpool A Etihad

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026
Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

July 18, 2026
Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

July 18, 2026
Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

July 18, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.