• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyin Warware Kalubalen Da Kiwon Kifi Ke Fuskanta A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Hanyoyin Warware Kalubalen Da Kiwon Kifi Ke Fuskanta A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Tarihin kiwon Kifi a Nijeriya, ya faro ne karkashin shirin kiwon Kifi na gwamnati a gonakin  Panyam da ke garin Jos  babban birnin Jihar Filato a shekarar 1951, inda a yanzu ake tafiyar da gonakin a matsayin masu zaman kansu.

Bincike ya nuna cewa, kiwon Kifi hanya ce guda daya tilo wadda za a iya cike gibin da ake da shi na karancinsa tare da kara yawan wanda ake kiwatawa a fadin wannan kasa.

  • An Gudanar Da Bikin Reel Africa A Birnin Shanghai
  • Gwamnatin Kano Ta Dawo Da Ma’aikatan Da Ta Dakatar Da Ganduje Ya Ɗauka Aiki

Sakamakon wannan bincike ne, ya sa Nijeriya ta shiga harkokin kiwon Kifi gadan-gadan, musamman saboda karancinsa da ake samu a manyan rafi; sakamakon yawan kamun sa da ake yi da kuma kara samun masu bukatarsa da suke karuwa a wannan kasa.

Bukatar da ake da ita ta Kifi a Nijeriya, an kiyasata ta kai ta tan miliyan 2.97 a duk shekara, sai dai ana iya samar da Kifin da ya kai kimanin tan miliyan 1.07 ne kawai a duk shekarar.

Wannan na nuna cewa, ana da gibin da ya kai na kimanin tan miliyan 1.9, wanda za a iya fitar da shi zuwa kasashen ketare, domin sama wa  Nijeriya kudin shiga; wanda akalla zai iya tasamma kimanin dala biliyan 1.2.

Hatta tan mliliyan 1.07 da ake samu a duk shekara, ana kuma samar da Kifi kimanin tan miliyan 313,231 ne kacal, inda kuma ake samar da sauran Kifin da ya kai kimanin tan miliyan 759,828 a duk shekara ta hanyar kiwata shi.

Har ila yau, wasu daga cikin hanyoyin da za a rage kalubale ko matsalolin kiwon kifin sun hada da samar Da Kudade, wanda ko shakka babu babban kalubale ne ga babban bankin Nijerya (CBN), ta hanyar shirin bayar da dauki daban-daban da yake bayarwa na kiwon Kifi, domin samun ribar da ta doshi naira biliyan 21.

Kazalika, ta hanyar shirin nan na bunkasa kaya na (CDI), babban bankin Nijeriya (CBN), ya rabar da kimanin naira miliyan 500 ga kamfanoni 40  da kuma wasu daga cikin masu kiwon Kifi sama da 3,000.

Babu shakka, wannan dauki ya taimaka wajen kara samar da kimanin tan 200 a duk shekara, inda kuma gwamnatin tarayya ta hanyar sauran shirye-shiyen ta tallafa wa masu kiwon Kifi wadanda ke a fadin wannan kasa.

Bugu da kari, ta hanyar bayar da rance ta bankunan ‘DMBs’, gwamnatin tarayya ta amince da bayar da bashi ga masu kiwon Kifin a Nijeriya, musamman domin su kara habaka sana’ar tasu.

Sai kuma batun samo ingantaccen Iri na Kifin da za a kiwata: Yana da matukar muhimmanci ga duk wanda zai fara kiwon Kifi, ya tabbatar ya samo ingantaccen Iri na Kifin da zai fara kiwatawa tare da samar da kyakkyawan yanayin da ya dace.

Don haka, ya kamata gwamnati ta samar da wuraren gudanar da yin bincike a fannin kiwon Kifi tare da samar da wadatattun kayan aiki, domin rika samar da ingantaccen Kifi a kasar nan.

Haka zalika, akwai batun samar da ingantaccen kwamin kiwon Kifin: Irin kwamin kiwon Kifin da ya fi dacewa masu kiwon su fi yin amfani da shi sun hada da; wanda aka gina, ma’ana wanda ake yi a cikin roba ko kuma wanda na tafi da gidanka da sauran makamantansu.

Sa’annan, batun kula da lafiyar Kifin da ake kiwatawa: Rashin kula da yadda ake kiwon Kifin da kuma rashin ciyar da su abinci, na haifar musu da barkewar annoba tare da mutuwa. Za a iya samun wannan nasara ta hanyar kafa gidan gonar kiwon Kifi a wuraren da ke da ruwa mai kyau da tsafta.

Sai kuma tabbatar da daidaitacciyar kasuwa: Gazawa wajen samar da tabbatacciyar kasuwa na daya daga cikin babban kalubalen da fannin kiwon Kifi ke fuskanta a wannan kasa.

Fannin kiwon Kifi kamar fannin sauran noma ne, wanda ba zai iya samun nasara ba, idan har ba a samar da ingattacciyar kasuwar da kamata ba, musamman domin kai wa ga abokan cinikayya.

Haka nan, batun samar da ingantattun hanyoyin safafar Kifin: Ana bukatar a samar da ingattattun hanyoyi, don yin jigilar Kifin daga gonakin da aka kiwata su zuwa guraren da za a sayar da su.

Saboda haka, ana bukatar gwamnati ta tabbatar da inganta hanyoyi, musamman domin a rage wa masu kiwon Kifin tsadar kashe kudaden yin jigilar da kuma rage musu asara, sakamakon rashin hanyoyi masu kyau.

Bugu da kari, batun samar da wajen adana Kifin, wato firji mai Inganci: Ana bukatar a samar da firjin da za a rika adana Kifin da za a yi jigilarsu, don gudun ka da su lalace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Afirka Na Bukatar Malaman Makaranta Miliyan 15 Nan Da 2030 -Patrick

Next Post

Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Ministar Harkokin Wajen Faransa

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 days ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 days ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 week ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 week ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Next Post
Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Ministar Harkokin Wajen Faransa

Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Ministar Harkokin Wajen Faransa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.