ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyin Warware Kalubalen Da Kiwon Kifi Ke Fuskanta A Nijeriya

by Abubakar Abba
3 years ago
Kifi

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Tarihin kiwon Kifi a Nijeriya, ya faro ne karkashin shirin kiwon Kifi na gwamnati a gonakin  Panyam da ke garin Jos  babban birnin Jihar Filato a shekarar 1951, inda a yanzu ake tafiyar da gonakin a matsayin masu zaman kansu.

Bincike ya nuna cewa, kiwon Kifi hanya ce guda daya tilo wadda za a iya cike gibin da ake da shi na karancinsa tare da kara yawan wanda ake kiwatawa a fadin wannan kasa.

  • An Gudanar Da Bikin Reel Africa A Birnin Shanghai
  • Gwamnatin Kano Ta Dawo Da Ma’aikatan Da Ta Dakatar Da Ganduje Ya Ɗauka Aiki

Sakamakon wannan bincike ne, ya sa Nijeriya ta shiga harkokin kiwon Kifi gadan-gadan, musamman saboda karancinsa da ake samu a manyan rafi; sakamakon yawan kamun sa da ake yi da kuma kara samun masu bukatarsa da suke karuwa a wannan kasa.

Bukatar da ake da ita ta Kifi a Nijeriya, an kiyasata ta kai ta tan miliyan 2.97 a duk shekara, sai dai ana iya samar da Kifin da ya kai kimanin tan miliyan 1.07 ne kawai a duk shekarar.

Wannan na nuna cewa, ana da gibin da ya kai na kimanin tan miliyan 1.9, wanda za a iya fitar da shi zuwa kasashen ketare, domin sama wa  Nijeriya kudin shiga; wanda akalla zai iya tasamma kimanin dala biliyan 1.2.

Hatta tan mliliyan 1.07 da ake samu a duk shekara, ana kuma samar da Kifi kimanin tan miliyan 313,231 ne kacal, inda kuma ake samar da sauran Kifin da ya kai kimanin tan miliyan 759,828 a duk shekara ta hanyar kiwata shi.

Har ila yau, wasu daga cikin hanyoyin da za a rage kalubale ko matsalolin kiwon kifin sun hada da samar Da Kudade, wanda ko shakka babu babban kalubale ne ga babban bankin Nijerya (CBN), ta hanyar shirin bayar da dauki daban-daban da yake bayarwa na kiwon Kifi, domin samun ribar da ta doshi naira biliyan 21.

Kazalika, ta hanyar shirin nan na bunkasa kaya na (CDI), babban bankin Nijeriya (CBN), ya rabar da kimanin naira miliyan 500 ga kamfanoni 40  da kuma wasu daga cikin masu kiwon Kifi sama da 3,000.

Babu shakka, wannan dauki ya taimaka wajen kara samar da kimanin tan 200 a duk shekara, inda kuma gwamnatin tarayya ta hanyar sauran shirye-shiyen ta tallafa wa masu kiwon Kifi wadanda ke a fadin wannan kasa.

Bugu da kari, ta hanyar bayar da rance ta bankunan ‘DMBs’, gwamnatin tarayya ta amince da bayar da bashi ga masu kiwon Kifin a Nijeriya, musamman domin su kara habaka sana’ar tasu.

Sai kuma batun samo ingantaccen Iri na Kifin da za a kiwata: Yana da matukar muhimmanci ga duk wanda zai fara kiwon Kifi, ya tabbatar ya samo ingantaccen Iri na Kifin da zai fara kiwatawa tare da samar da kyakkyawan yanayin da ya dace.

Don haka, ya kamata gwamnati ta samar da wuraren gudanar da yin bincike a fannin kiwon Kifi tare da samar da wadatattun kayan aiki, domin rika samar da ingantaccen Kifi a kasar nan.

Haka zalika, akwai batun samar da ingantaccen kwamin kiwon Kifin: Irin kwamin kiwon Kifin da ya fi dacewa masu kiwon su fi yin amfani da shi sun hada da; wanda aka gina, ma’ana wanda ake yi a cikin roba ko kuma wanda na tafi da gidanka da sauran makamantansu.

Sa’annan, batun kula da lafiyar Kifin da ake kiwatawa: Rashin kula da yadda ake kiwon Kifin da kuma rashin ciyar da su abinci, na haifar musu da barkewar annoba tare da mutuwa. Za a iya samun wannan nasara ta hanyar kafa gidan gonar kiwon Kifi a wuraren da ke da ruwa mai kyau da tsafta.

Sai kuma tabbatar da daidaitacciyar kasuwa: Gazawa wajen samar da tabbatacciyar kasuwa na daya daga cikin babban kalubalen da fannin kiwon Kifi ke fuskanta a wannan kasa.

Fannin kiwon Kifi kamar fannin sauran noma ne, wanda ba zai iya samun nasara ba, idan har ba a samar da ingattacciyar kasuwar da kamata ba, musamman domin kai wa ga abokan cinikayya.

Haka nan, batun samar da ingantattun hanyoyin safafar Kifin: Ana bukatar a samar da ingattattun hanyoyi, don yin jigilar Kifin daga gonakin da aka kiwata su zuwa guraren da za a sayar da su.

Saboda haka, ana bukatar gwamnati ta tabbatar da inganta hanyoyi, musamman domin a rage wa masu kiwon Kifin tsadar kashe kudaden yin jigilar da kuma rage musu asara, sakamakon rashin hanyoyi masu kyau.

Bugu da kari, batun samar da wajen adana Kifin, wato firji mai Inganci: Ana bukatar a samar da firjin da za a rika adana Kifin da za a yi jigilarsu, don gudun ka da su lalace.

Kifi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Ministar Harkokin Wajen Faransa

Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Ministar Harkokin Wajen Faransa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.