• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uba Sani Ya Baiwa Wadanda Suka Lashe Musabakar Karatun Alkur’ani Kujerun Hajji

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Uba Sani Ya Baiwa Wadanda Suka Lashe Musabakar Karatun Alkur’ani Kujerun Hajji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya bayyana kyautar kujerar aikin Hajji ga zakarun (Mace da Namiji) da suka lashe musabakar karatun Alkur’ani ta shekara-shekara a jihar Kaduna.

Gwamnan wanda ya halarci rufe musabakar a filin musabaka na Dr. Ahmad Muhammad makarfi quranic recitation complex, kinkinau/’yantukwane, Kaduna a ranar Asabar ya kuma bayar da kyautar kudi ga wadanda suka lashe gasar daga matsayi na daya zuwa na biyar a rukuni daban-daban na gasar.

  • Minista Ya Biya Tarar Naira Miliyan 585 Domin A Saki Daurarru 4,068
  • Sojoji Da ‘Yan banga Sun Ceto Mutum 6 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kebbi

Da yake karin haske game da aikin Hajji na 2024, Gwamnan ya ce, ya kaddamar da kwamitin da zai tabbatar da cewa, aikin Hajjin badi bai fuska kalubale ba kamar yadda na bara ya ci karo da kalubale daban-daban. Alhazai sun gamu da damuwa daga bangaren abinci, masaukai da sauransu.

Ya yi nuni da cewa, mutane da dama sun tuntube shi domin neman kwangilar ayyukan aikin Hajji kamar kayan sawar alhazai da abinci da wurin kwana da sauransu.

“Abin da nake so na gaya wa duk wanda ya samu kwangilar aikin Hajji, shi ne ya ji tsoron Allah, kuma ya bai wa alhazai abin da ya dace domin su samu kyawawan addu’o’in alhazai ba na fushinsu ba. ” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

Yayin da yake magana kan mahimmancin Alkur’ani mai girma, Gwamna Sani ya ce, al’umma za su samu zaman lafiya idan dukkan musulmi suka rika karanta Alkur’ani a kai a kai tare da bin koyarwarsa, ya ce za a magance yawancin kalubalen da ake fuskanta a kasar nan.

Tunda farko, da yake gabatar da fadakarwa a wajen taron, Jagoran kungiyar Jama’atu Izalatu Bid’ah Wa Ikamatu Sunnah (JIBWIS) ta kasa, Sheikh Abdullahi Bala Lau, ya ce, Alkur’ani shi ne wanda duk al’ummar musulmi ta tafi akai kuma bata da wani bambancin ra’ayi akansa.

Don haka, ya bukaci al’ummar musulmi musamman malamai da su koma ga Alkur’ani su karantar da shi ga sauran jama’a, yana mai cewa, itace hanya mai sauki wajen dorewar zaman lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin HajjiGwamna Uba SaniJIBWIS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Zai Yiwu A Kori Manchester City Da Liverpool Daga Gasar Firimiya?

Next Post

Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

9 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

11 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

13 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

15 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

16 hours ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

17 hours ago
Next Post
Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas

Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Musabaka

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.