• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Hada Guiwa Da Hukumomi Don Yaki Da Ta’ammuli Da Miyagun Kwayoyi A Tsakanin ‘Yan Mata – Shugabar MWAN

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
MWAN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabar kungiyar Mata Daktoci ta jihar Kaduna kuma ta Kasa (Mai jiran gado), MWAN, Dr. Zainab Muhammad Idris Kwaru ta bayyana cewa, Kungiyar a karkashin jagorancinta za ta maida hankali wajen yaki da ta’ammuli da miyagun kwayoyi ta hanyar hadin guiwa da hukumomin da lamarin ya shafa.

Dr. Kwaru, ta bayyana hakan ne yayin da kungiyar ta kai ziyarar girmamawa ga Mataimakiyar Gwamna Jihar Kaduna, Dr. Hadiza Balarabe Sabuwa a dakin taro da ke gidan gwamnatin jihar a ranar Alhamis 30 ga watan Nuwamba 2023.

  • Dumamar Yanayi Ta Haddasa Ruwan Saman Ba-zata A Arewa – NiMet
  • Shi Mai Kula Da Babban Aiki Ne 

Tun da farko, Dr. Hadiza Balarabe sabuwa ta nuna farin cikinta na yadda kungiyar ta girmamata ta kawo mata ziyara har gidan Gwamnatin, inda ta ce, itama Mamba ce a kungiyar ta MWAN.

“Babban abinda nafi son kungiyarmu ta mayar da hankali shi ne, la’akari da yadda za a dakile yawaitar ta’ammuli da miyagun kwayoyi a tsakanin ‘yan mata da yaranmu.

“Ya dace, mu kara fadada tunaninmu ta hanyar hadin guiwa da hukumomin da suka dace, kamar NDLEA, don shawo kan wannan kalubale. Hatsari ne babba cikin al’umma, mace tana shaye-shaye, sabida itace uwa mai tarbiyyantar da ‘ya’yanta da al’umma.” Inji Dr. Balarabe.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

A nata jawabin, Dr. Zainab Muhammad Kwaru, ta bayyana cewa, Makasudin ziyarar kungiyar itace, kawo gaisuwa ga mai girma mataimakiyar gwamnan jihar Kaduna, Dr. Hadiza Balarabe sabuwa sannan kuma mu bayyana mata nasarar da muka samu, na zabenmu a matsayin shugabar kungiyar mata daktoci ta kasa, kuma mu nuna mata mun yaba da gudunmawar da ta ba mu na daga lokutanta da kudade da muka yi amfani da su na ganin mun samu wannan nasarar.

Daga nan ne, Dr. Kwaru ta zayyana wa manema labarai wasu daga cikin muhimman shirye-shiryen da kungiyar ke gudanarwa a baya da wadanda take kokarin shiryawa a nan gaba, inda tace, sun hada da shiga cikin al’umma mu bada gudunmawarmu na duba lafiya da basu kulawa na musamman, idan har akwai bukatar tura su manyan asibiti, sai mu yi hakan.

Akwai asibitoci na unguwanni da muka sa mambobinmu suna ziyarta don bada gudunmawa na duba marasa lafiya, muna fadakarwa da wayar da kai acikin al’umma daga bangaren kiwon lafiyar Yara da Mata masu juna-biyu. Wasu lokuta, muna kai kayayyakin agaji ga gidajen kaso ko na gajiyayyu ko na Marayu.

Da take mayar da martani kan batun Mataimakiyar Gwamna na dakile yawaitar ta’ammuli da miyagun kwayoyi a tsakanin yara Mata, Dr. Zainab ta bayyana cewa, daga bangarensu, suna amfani da mambobinsu da ke da kwarewa a fannin kwakwalwa, suna fadakarwa da wayar da kai kan illar ta’ammuli da miyagun kwayoyi.

Ta bayyana cewa, akwai damuwa matuka ganin yadda yara Mata yanzun ke ta’ammuli da miyagun kwayoyi, ganin cewa, itace uwa mai tarbiyyantar da ‘ya’yanta da al’umma baki daya. Lallai wannan barazana ce babba acikin al’ummarmu.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin KadunaMWAN
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattalin Arzikin Nijeriya Zai Farfado Nan Da Wata 15 – Shettima

Next Post

Faransa Ta Nemi Karin Gurbin Kasuwanci Da Nijeriya

Related

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

10 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

11 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

12 hours ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

15 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

17 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

18 hours ago
Next Post
Faransa Ta Nemi Karin Gurbin Kasuwanci Da Nijeriya

Faransa Ta Nemi Karin Gurbin Kasuwanci Da Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.