ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Hada Guiwa Da Hukumomi Don Yaki Da Ta’ammuli Da Miyagun Kwayoyi A Tsakanin ‘Yan Mata – Shugabar MWAN

by Sulaiman
3 years ago
MWAN

Shugabar kungiyar Mata Daktoci ta jihar Kaduna kuma ta Kasa (Mai jiran gado), MWAN, Dr. Zainab Muhammad Idris Kwaru ta bayyana cewa, Kungiyar a karkashin jagorancinta za ta maida hankali wajen yaki da ta’ammuli da miyagun kwayoyi ta hanyar hadin guiwa da hukumomin da lamarin ya shafa.

Dr. Kwaru, ta bayyana hakan ne yayin da kungiyar ta kai ziyarar girmamawa ga Mataimakiyar Gwamna Jihar Kaduna, Dr. Hadiza Balarabe Sabuwa a dakin taro da ke gidan gwamnatin jihar a ranar Alhamis 30 ga watan Nuwamba 2023.

  • Dumamar Yanayi Ta Haddasa Ruwan Saman Ba-zata A Arewa – NiMet
  • Shi Mai Kula Da Babban Aiki Ne 

Tun da farko, Dr. Hadiza Balarabe sabuwa ta nuna farin cikinta na yadda kungiyar ta girmamata ta kawo mata ziyara har gidan Gwamnatin, inda ta ce, itama Mamba ce a kungiyar ta MWAN.

ADVERTISEMENT

“Babban abinda nafi son kungiyarmu ta mayar da hankali shi ne, la’akari da yadda za a dakile yawaitar ta’ammuli da miyagun kwayoyi a tsakanin ‘yan mata da yaranmu.

“Ya dace, mu kara fadada tunaninmu ta hanyar hadin guiwa da hukumomin da suka dace, kamar NDLEA, don shawo kan wannan kalubale. Hatsari ne babba cikin al’umma, mace tana shaye-shaye, sabida itace uwa mai tarbiyyantar da ‘ya’yanta da al’umma.” Inji Dr. Balarabe.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

A nata jawabin, Dr. Zainab Muhammad Kwaru, ta bayyana cewa, Makasudin ziyarar kungiyar itace, kawo gaisuwa ga mai girma mataimakiyar gwamnan jihar Kaduna, Dr. Hadiza Balarabe sabuwa sannan kuma mu bayyana mata nasarar da muka samu, na zabenmu a matsayin shugabar kungiyar mata daktoci ta kasa, kuma mu nuna mata mun yaba da gudunmawar da ta ba mu na daga lokutanta da kudade da muka yi amfani da su na ganin mun samu wannan nasarar.

Daga nan ne, Dr. Kwaru ta zayyana wa manema labarai wasu daga cikin muhimman shirye-shiryen da kungiyar ke gudanarwa a baya da wadanda take kokarin shiryawa a nan gaba, inda tace, sun hada da shiga cikin al’umma mu bada gudunmawarmu na duba lafiya da basu kulawa na musamman, idan har akwai bukatar tura su manyan asibiti, sai mu yi hakan.

Akwai asibitoci na unguwanni da muka sa mambobinmu suna ziyarta don bada gudunmawa na duba marasa lafiya, muna fadakarwa da wayar da kai acikin al’umma daga bangaren kiwon lafiyar Yara da Mata masu juna-biyu. Wasu lokuta, muna kai kayayyakin agaji ga gidajen kaso ko na gajiyayyu ko na Marayu.

Da take mayar da martani kan batun Mataimakiyar Gwamna na dakile yawaitar ta’ammuli da miyagun kwayoyi a tsakanin yara Mata, Dr. Zainab ta bayyana cewa, daga bangarensu, suna amfani da mambobinsu da ke da kwarewa a fannin kwakwalwa, suna fadakarwa da wayar da kai kan illar ta’ammuli da miyagun kwayoyi.

Ta bayyana cewa, akwai damuwa matuka ganin yadda yara Mata yanzun ke ta’ammuli da miyagun kwayoyi, ganin cewa, itace uwa mai tarbiyyantar da ‘ya’yanta da al’umma baki daya. Lallai wannan barazana ce babba acikin al’ummarmu.

 

MWAN
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Faransa Ta Nemi Karin Gurbin Kasuwanci Da Nijeriya

Faransa Ta Nemi Karin Gurbin Kasuwanci Da Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.