ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Hada Guiwa Da Hukumomi Don Yaki Da Ta’ammuli Da Miyagun Kwayoyi A Tsakanin ‘Yan Mata – Shugabar MWAN

by Sulaiman
3 years ago
MWAN

Shugabar kungiyar Mata Daktoci ta jihar Kaduna kuma ta Kasa (Mai jiran gado), MWAN, Dr. Zainab Muhammad Idris Kwaru ta bayyana cewa, Kungiyar a karkashin jagorancinta za ta maida hankali wajen yaki da ta’ammuli da miyagun kwayoyi ta hanyar hadin guiwa da hukumomin da lamarin ya shafa.

Dr. Kwaru, ta bayyana hakan ne yayin da kungiyar ta kai ziyarar girmamawa ga Mataimakiyar Gwamna Jihar Kaduna, Dr. Hadiza Balarabe Sabuwa a dakin taro da ke gidan gwamnatin jihar a ranar Alhamis 30 ga watan Nuwamba 2023.

  • Dumamar Yanayi Ta Haddasa Ruwan Saman Ba-zata A Arewa – NiMet
  • Shi Mai Kula Da Babban Aiki Ne 

Tun da farko, Dr. Hadiza Balarabe sabuwa ta nuna farin cikinta na yadda kungiyar ta girmamata ta kawo mata ziyara har gidan Gwamnatin, inda ta ce, itama Mamba ce a kungiyar ta MWAN.

ADVERTISEMENT

“Babban abinda nafi son kungiyarmu ta mayar da hankali shi ne, la’akari da yadda za a dakile yawaitar ta’ammuli da miyagun kwayoyi a tsakanin ‘yan mata da yaranmu.

“Ya dace, mu kara fadada tunaninmu ta hanyar hadin guiwa da hukumomin da suka dace, kamar NDLEA, don shawo kan wannan kalubale. Hatsari ne babba cikin al’umma, mace tana shaye-shaye, sabida itace uwa mai tarbiyyantar da ‘ya’yanta da al’umma.” Inji Dr. Balarabe.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

A nata jawabin, Dr. Zainab Muhammad Kwaru, ta bayyana cewa, Makasudin ziyarar kungiyar itace, kawo gaisuwa ga mai girma mataimakiyar gwamnan jihar Kaduna, Dr. Hadiza Balarabe sabuwa sannan kuma mu bayyana mata nasarar da muka samu, na zabenmu a matsayin shugabar kungiyar mata daktoci ta kasa, kuma mu nuna mata mun yaba da gudunmawar da ta ba mu na daga lokutanta da kudade da muka yi amfani da su na ganin mun samu wannan nasarar.

Daga nan ne, Dr. Kwaru ta zayyana wa manema labarai wasu daga cikin muhimman shirye-shiryen da kungiyar ke gudanarwa a baya da wadanda take kokarin shiryawa a nan gaba, inda tace, sun hada da shiga cikin al’umma mu bada gudunmawarmu na duba lafiya da basu kulawa na musamman, idan har akwai bukatar tura su manyan asibiti, sai mu yi hakan.

Akwai asibitoci na unguwanni da muka sa mambobinmu suna ziyarta don bada gudunmawa na duba marasa lafiya, muna fadakarwa da wayar da kai acikin al’umma daga bangaren kiwon lafiyar Yara da Mata masu juna-biyu. Wasu lokuta, muna kai kayayyakin agaji ga gidajen kaso ko na gajiyayyu ko na Marayu.

Da take mayar da martani kan batun Mataimakiyar Gwamna na dakile yawaitar ta’ammuli da miyagun kwayoyi a tsakanin yara Mata, Dr. Zainab ta bayyana cewa, daga bangarensu, suna amfani da mambobinsu da ke da kwarewa a fannin kwakwalwa, suna fadakarwa da wayar da kai kan illar ta’ammuli da miyagun kwayoyi.

Ta bayyana cewa, akwai damuwa matuka ganin yadda yara Mata yanzun ke ta’ammuli da miyagun kwayoyi, ganin cewa, itace uwa mai tarbiyyantar da ‘ya’yanta da al’umma baki daya. Lallai wannan barazana ce babba acikin al’ummarmu.

 

MWAN
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Faransa Ta Nemi Karin Gurbin Kasuwanci Da Nijeriya

Faransa Ta Nemi Karin Gurbin Kasuwanci Da Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.