• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Majalisar Dinkin Duniya Ta Kammala Shirin Yaki Da Cin Zarafin Mata A Nijeriya

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Majalisar Dinkin Duniya Ta Kammala Shirin Yaki Da Cin Zarafin Mata A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya tare da hadin gwaiar Tarayyar Turai da sauran takwarorinsu sun kamala wani shirin yaki da cin zarafin mata a Nijeriya mai lakabin ‘spotlight initiatibe’ tare da mika ragamar cibiyoyin gudanar da aikin ga gwamnatin Nijeriya.

An kamala shirin ne a otel na Transcorp da ke Abuja a tsakiyar makon nan inda wasu ministoci da shugabannin hukumomin gwamnati suka halarta.

  • Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024
  • Kamfanonin Siminti Ke Haifar Da Kashi 7 Na Dumamar Yanayi A Duniya – Dangote

A jawaban da suka gudanar daban-daban, Babban Jami’in Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya, Mattias Schmale da Wakiliyar Tarayyar Turai a Nijeriya da ECOWAS, Samuela Isopi sun ce shirin ya samu nasara bisa yadda yake bai wa matan da aka ci zarafi damar zuwa cibiyoyin kulawa don sake farfado da rayuwarsu, kana suka ce mika shirin daga gwamnati ne zuwa gwamnati kasancewar su goyon baya suka bayar amma gwamnati ce ta aiwatar da shirin.

Da yake jawabi, Ministan Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Atiku Bagudu wanda Dr. Lare Akanye ya wakilta, ya bayyana cewa, “An samu ci gaba a yaki da cin zarafin mata tun daga lokacin da aka kaddamar a 2018. Akwai cibiyoyi daban-daban da aka samar a wasu sassa na kasa domin gudanar da aikace-aikacen da suka shafi ceto rayukan wadanda aka ci zarafinsu da kuma sake farfado da rayuwarsu

“Gwamnati za ta yi dukkan mai yiwuwa wurin bayar da goyon baya ga dukkan ire-iren wadannan shirye-shirye na ci gaban rayuwar ‘yan kasa. Kuma ya yaba wa Tarayyar Turai da ta bayar da kashi 5 cikin 100 na taimakon kudin da ta ware a duniya inda Nijeriya take cin gajiyar wajen miliyan 500.” In ji shi

Labarai Masu Nasaba

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

Hakazalika, Ministan Shari’a, Fagbemi Lateef ya bayyana cewa, ya yi magana da kungiyar gwamnoni domin fadada tsare-tsare da shirye-shiryen da tarayya ke gabatarwa game da yaki da cin zarafin mata.

Yanzu haka, a cewarsa, ma’aikatarsa ta mike haikan wurin ganin ana hukunta duk wadanda aka kama suna cin zarafin mata, “yanzu haka akwai shirin da muka yi na tabbatar da cewa ana hukunta masu cin zarafin mata a makarantu. Za mu tabbatar da kare ‘yancin wadanda al’amarin ya rutsa da su da kuma tabbatar da cewa wadanda suka aikata sun gurfana a gaban kuliya.

“Muna jin dadin cewa a yau da ake rufe wannan shiri na yaki da cin zarafin mata na ‘Spotlight Initiatib’e, an samu ci gaba a kan manufar shirin kuma Wannan ya kara nuna cewa idan muka yi kawance da abokan ci gaba, za mu samar da sauyi mai ma’ana ga rayuwar al’umma.”

Shi ma a jawabinsa, Sarkin Shonga, Dr. Haliru Yahaya Ndanusa, ya bukaci al’umma su hada karfi da karfe wajen kawar da dukkan wani nau’i na cin zarafin mata domin kyautata rayuwarsu.

Ya ba da misalin cewa matukar aka bari cin zarafin mata ya ci gaba da gudana to babu shakka za a zare musu walwala a rayuwarsu inda hakan kuma zai shafi hatta ci gaban kasa saboda mata masu ilimi da ke cikin kwanciyar hankali suna ba da gudunmawa ga ciyar da kasa gaba.

Shi kuwa Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya, Kayode Egbetokun wanda DIG Amina ta wakilta, ya nunar da cewa, ‘Yansanda ne ke jagorantar yaki da duk wani nau’i na cin zarafin mata kuma za su ci gaba da tabbatar da fatattakar duk wadanda suka dauki cin zarafin mata dabi’a.

Har ila yau, ya ce rundunar ta samar da sashe na musamman a kan kare hakkin mata a daukacin jihohi 36 har da Abuja. Kuma za su ci gaba da kai daukin gaggawa duk lokacin da aka kira su domin kai agaji ga matan da aka ci zarafinsu.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana da shirin sun yi bayanin yadda rayuwarsu ta kasance a baya da kuma a yanzu, kana masu wasan kwaikwayo suka nishadantar da fadakar da mutane game da muhimmancin taimaka wa matan da aka ci zarafinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Zan Yi Katsalandan A Gwamnatin Ododo Ba – Yahaya Bello

Next Post

Duk Likitan Mata Na Kula Da Mara Lafiya 6,000 Maimakon 400 A Nijeriya -SOGON

Related

Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu
Manyan Labarai

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

1 hour ago
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya
Labarai

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

7 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

18 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

19 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

20 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

1 day ago
Next Post
Duk Likitan Mata Na Kula Da Mara Lafiya 6,000 Maimakon 400 A Nijeriya -SOGON

Duk Likitan Mata Na Kula Da Mara Lafiya 6,000 Maimakon 400 A Nijeriya -SOGON

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.