• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Hana ‘Yan Boko Haram Mayar Da Jihar Neja Hedikwatarsu – Tsohon Gwamnan Jihar 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Na Hana ‘Yan Boko Haram Mayar Da Jihar Neja Hedikwatarsu – Tsohon Gwamnan Jihar 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan jihar Neja, Dr. Muazu Babangida Aliyu, ya bayyana yadda ya fatattaki shugabannin kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau da Abu Qaqa, daga jihar Neja a wa’adinsa na farko a matsayin gwamnan jihar, inda ya ce, sun shirya mayar da jihar Hedikwatarsu.

Ya ce, shirin magance kalubalen tsaro da ke addabar Nijeriya, kamar ta’addanci da fashi da makami, shiri ne da yake bukatar tanadi mai zurfi ta hanyar kawar da adadin yara miliyan 20 da ba su zuwa makaranta su koma makaranta domin ceto Nijeriya daga matsayin kasa mafi talauci nan gaba.

  • Yadda Matakin Raya Kauyuka Da Sin Ta Dauka Ke Taimakawa Kawar Da Talauci Da Ma Yayata Aladun Kasar
  • Shirin Rage Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Biyan Sabon Tsarin Albashi Daga Afrilun 2024 – Minista

Dr. Aliyu ya bayyana haka ne a jihar Kaduna a karshen mako lokacin da ya bayyana a matsayin babban bako mai jawabi na shekara ta 2023, wanda cibiyar hulda da jama’a ta Nijeriya (NIPR), reshen Jihar Kaduna ta shirya.

Tsohon gwamnan ya ce, “Babban manufar gwamnati ita ce tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasarta, wanda mafi yawan gwamnonin jihohi ba sa daukarsa da muhimmanci. A matsayinka na Babban Jami’in Tsaro na jiharka, bai dace ka yi da’awar gazawa kan tsaron mutananka ba. Eh, mai yiwuwa ne jami’an hukumomin tsaro da ake turowa ba daga jiharka suka fito ba, jami’an gwamnatin tarayya ne da aka turo domin su taimaka wa jiharka.

“Kasancewarka shugaba mai kishin jama’arka, yana taimakawa sosai. A lokacin da na zama Gwamnan jihar Neja, na samu kalubalen tsaro ta hanyar wasu mutane tara da suka je wani kauye a karamar hukumar Mokwa, wadanda suka ninka a shekarar 2007 zuwa mutum 7,000 kuma suna yin fashi da makami da sace mata a yankin. Nan da nan Suka zama wata babbar runduna.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

“Na kuma gano cewa wasu gwamnoni (makwabtan Neja) da dama sun yi kokarin yin wani abu akan lamarin amma wata kila suna shakkar tunkarar Shugaban kasa. Hasali ma, jami’an hukumar shige-da-fice guda biyu da aka turo domin su binciki ayyukan kungiyar, sun rikide sun zama mambobin kungiyar. Lokacin da muka gudanar da bincike, sai muka gano cewa sama da kashi 60 cikin 100 na ‘yan kungiyar ba ‘yan Nijeriya ba ne. Asalin Shekau da Abu Qaga su ne shugabannin kungiyar. Na samu goyon bayan Marigayi Shugaban Kasa, Musa Yar’adua cewa, mu maida kowa garinshi sannan aka kai ‘yan kasashen waje iyakokin kasashensu.

“Kila wannan matakin ne ya ceto jihar Neja daga zama tushen Boko Haram. Kamar yadda muka sani, suna ziyartar gadar kogin Neja akai-akai. Babu shakka Gwamnatin Tarayya za ta goyi bayan duk wani Gwamna da ya ke kokarin sauke nauyin da ke wuyansa na kare rayuka da dukiyoyin al’umma” Inji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramNejaSambisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Kwallon Kano Pillars Ya Zazzaga Kwallaye Biyar A Ragar Gombe United 

Next Post

Atiku Ya Musanta Amfana Da Maido Da Lasisin Kamfanin Intels Da Gwamnati Ta Yi

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

3 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

4 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

5 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

7 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

9 hours ago
Next Post
Atiku Ya Musanta Amfana Da Maido Da Lasisin Kamfanin Intels Da Gwamnati Ta Yi

Atiku Ya Musanta Amfana Da Maido Da Lasisin Kamfanin Intels Da Gwamnati Ta Yi

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.