ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Hana ‘Yan Boko Haram Mayar Da Jihar Neja Hedikwatarsu – Tsohon Gwamnan Jihar 

by Sulaiman
3 years ago
Boko Haram

Tsohon gwamnan jihar Neja, Dr. Muazu Babangida Aliyu, ya bayyana yadda ya fatattaki shugabannin kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau da Abu Qaqa, daga jihar Neja a wa’adinsa na farko a matsayin gwamnan jihar, inda ya ce, sun shirya mayar da jihar Hedikwatarsu.

Ya ce, shirin magance kalubalen tsaro da ke addabar Nijeriya, kamar ta’addanci da fashi da makami, shiri ne da yake bukatar tanadi mai zurfi ta hanyar kawar da adadin yara miliyan 20 da ba su zuwa makaranta su koma makaranta domin ceto Nijeriya daga matsayin kasa mafi talauci nan gaba.

  • Yadda Matakin Raya Kauyuka Da Sin Ta Dauka Ke Taimakawa Kawar Da Talauci Da Ma Yayata Aladun Kasar
  • Shirin Rage Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Biyan Sabon Tsarin Albashi Daga Afrilun 2024 – Minista

Dr. Aliyu ya bayyana haka ne a jihar Kaduna a karshen mako lokacin da ya bayyana a matsayin babban bako mai jawabi na shekara ta 2023, wanda cibiyar hulda da jama’a ta Nijeriya (NIPR), reshen Jihar Kaduna ta shirya.

ADVERTISEMENT

Tsohon gwamnan ya ce, “Babban manufar gwamnati ita ce tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasarta, wanda mafi yawan gwamnonin jihohi ba sa daukarsa da muhimmanci. A matsayinka na Babban Jami’in Tsaro na jiharka, bai dace ka yi da’awar gazawa kan tsaron mutananka ba. Eh, mai yiwuwa ne jami’an hukumomin tsaro da ake turowa ba daga jiharka suka fito ba, jami’an gwamnatin tarayya ne da aka turo domin su taimaka wa jiharka.

“Kasancewarka shugaba mai kishin jama’arka, yana taimakawa sosai. A lokacin da na zama Gwamnan jihar Neja, na samu kalubalen tsaro ta hanyar wasu mutane tara da suka je wani kauye a karamar hukumar Mokwa, wadanda suka ninka a shekarar 2007 zuwa mutum 7,000 kuma suna yin fashi da makami da sace mata a yankin. Nan da nan Suka zama wata babbar runduna.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Na kuma gano cewa wasu gwamnoni (makwabtan Neja) da dama sun yi kokarin yin wani abu akan lamarin amma wata kila suna shakkar tunkarar Shugaban kasa. Hasali ma, jami’an hukumar shige-da-fice guda biyu da aka turo domin su binciki ayyukan kungiyar, sun rikide sun zama mambobin kungiyar. Lokacin da muka gudanar da bincike, sai muka gano cewa sama da kashi 60 cikin 100 na ‘yan kungiyar ba ‘yan Nijeriya ba ne. Asalin Shekau da Abu Qaga su ne shugabannin kungiyar. Na samu goyon bayan Marigayi Shugaban Kasa, Musa Yar’adua cewa, mu maida kowa garinshi sannan aka kai ‘yan kasashen waje iyakokin kasashensu.

“Kila wannan matakin ne ya ceto jihar Neja daga zama tushen Boko Haram. Kamar yadda muka sani, suna ziyartar gadar kogin Neja akai-akai. Babu shakka Gwamnatin Tarayya za ta goyi bayan duk wani Gwamna da ya ke kokarin sauke nauyin da ke wuyansa na kare rayuka da dukiyoyin al’umma” Inji shi.

Boko Haram
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Atiku Ya Musanta Amfana Da Maido Da Lasisin Kamfanin Intels Da Gwamnati Ta Yi

Atiku Ya Musanta Amfana Da Maido Da Lasisin Kamfanin Intels Da Gwamnati Ta Yi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.