ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Hana ‘Yan Boko Haram Mayar Da Jihar Neja Hedikwatarsu – Tsohon Gwamnan Jihar 

by Sulaiman
3 years ago
Boko Haram

Tsohon gwamnan jihar Neja, Dr. Muazu Babangida Aliyu, ya bayyana yadda ya fatattaki shugabannin kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau da Abu Qaqa, daga jihar Neja a wa’adinsa na farko a matsayin gwamnan jihar, inda ya ce, sun shirya mayar da jihar Hedikwatarsu.

Ya ce, shirin magance kalubalen tsaro da ke addabar Nijeriya, kamar ta’addanci da fashi da makami, shiri ne da yake bukatar tanadi mai zurfi ta hanyar kawar da adadin yara miliyan 20 da ba su zuwa makaranta su koma makaranta domin ceto Nijeriya daga matsayin kasa mafi talauci nan gaba.

  • Yadda Matakin Raya Kauyuka Da Sin Ta Dauka Ke Taimakawa Kawar Da Talauci Da Ma Yayata Aladun Kasar
  • Shirin Rage Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Biyan Sabon Tsarin Albashi Daga Afrilun 2024 – Minista

Dr. Aliyu ya bayyana haka ne a jihar Kaduna a karshen mako lokacin da ya bayyana a matsayin babban bako mai jawabi na shekara ta 2023, wanda cibiyar hulda da jama’a ta Nijeriya (NIPR), reshen Jihar Kaduna ta shirya.

ADVERTISEMENT

Tsohon gwamnan ya ce, “Babban manufar gwamnati ita ce tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasarta, wanda mafi yawan gwamnonin jihohi ba sa daukarsa da muhimmanci. A matsayinka na Babban Jami’in Tsaro na jiharka, bai dace ka yi da’awar gazawa kan tsaron mutananka ba. Eh, mai yiwuwa ne jami’an hukumomin tsaro da ake turowa ba daga jiharka suka fito ba, jami’an gwamnatin tarayya ne da aka turo domin su taimaka wa jiharka.

“Kasancewarka shugaba mai kishin jama’arka, yana taimakawa sosai. A lokacin da na zama Gwamnan jihar Neja, na samu kalubalen tsaro ta hanyar wasu mutane tara da suka je wani kauye a karamar hukumar Mokwa, wadanda suka ninka a shekarar 2007 zuwa mutum 7,000 kuma suna yin fashi da makami da sace mata a yankin. Nan da nan Suka zama wata babbar runduna.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

“Na kuma gano cewa wasu gwamnoni (makwabtan Neja) da dama sun yi kokarin yin wani abu akan lamarin amma wata kila suna shakkar tunkarar Shugaban kasa. Hasali ma, jami’an hukumar shige-da-fice guda biyu da aka turo domin su binciki ayyukan kungiyar, sun rikide sun zama mambobin kungiyar. Lokacin da muka gudanar da bincike, sai muka gano cewa sama da kashi 60 cikin 100 na ‘yan kungiyar ba ‘yan Nijeriya ba ne. Asalin Shekau da Abu Qaga su ne shugabannin kungiyar. Na samu goyon bayan Marigayi Shugaban Kasa, Musa Yar’adua cewa, mu maida kowa garinshi sannan aka kai ‘yan kasashen waje iyakokin kasashensu.

“Kila wannan matakin ne ya ceto jihar Neja daga zama tushen Boko Haram. Kamar yadda muka sani, suna ziyartar gadar kogin Neja akai-akai. Babu shakka Gwamnatin Tarayya za ta goyi bayan duk wani Gwamna da ya ke kokarin sauke nauyin da ke wuyansa na kare rayuka da dukiyoyin al’umma” Inji shi.

Boko Haram
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Atiku Ya Musanta Amfana Da Maido Da Lasisin Kamfanin Intels Da Gwamnati Ta Yi

Atiku Ya Musanta Amfana Da Maido Da Lasisin Kamfanin Intels Da Gwamnati Ta Yi

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.