• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya yi tir da Allah wadai da kisan da sojoji suka yi wa masu maulidi da cewa hakan kan ya faru ne bisa ‘kuskure’, inda ya misalta hakan da babban sakacin da bai kamata ya faru ba. 

Dahiru Bauchi a saƙon jajensa da ya aike wa musulman duniya kan kisan masu Maulidi kauyen Tudun Biri da ke ƙaramar hukumar Igabi a Kaduna da ake zargin mutum kusan 85 sun rasa rayukansu yayin da wasu sama da 50 suka jikkata a daren ranar Lahadi yayin da suke zaman tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad wato Maulidi.

  • Taron SGI Na Gudana Kan Sauyin Yanayi Karo Na 28
  • Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan N207.75bn A Matsayin Kasafin 2024

Shehin ya bukaci gwamnati da ta gabbata kafa kwamitin bincike da zai gano waɗanda suka aikata hakan domin hukunta su.

A cewarsa, koda sojojin sama sun ce ba su da masaniya kan kisan, amma alhakin kula da yaƙi ta sama na wuyarsu don haka su ma akwai sakacinsu, ya kuma dora laifin ga sojojin sama da na kasa da kuma gwamnati.

Kazalika, babban malamin darikar ya nemi gwamnati ta biya diyyar masu maulidin da suka rasa rayukansu sakamakon ruwan bama-bamai da sojoji suka yi musu.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

A cewarsa: “Ina yin ta’aziyya ga dukkanin musuluman duniya da musulman Afrika da musulman Nijeriya a kan abun da ya faru, wanda ya faru a Kaduna mun bincika sun ce wai ba jiragen saman sojojin Nijeriya ba ne, sojojin kasan Nijeriya ko sun ce su ne, to ai su babu dama su hau sama. Saboda haka mun yi mamakin yadda aka rasa rayuka.”

Ya ce, babban mai laifi kan wannan lamarin ita ce gwamnati domin ita ce ta yi sake.

“Haƙiƙa mun ji zafi! mun ji zafi!! kuma muna yin ta’aziyya ga dukkanin musulmai na duniya bisa ga wannan rashin da muka yi.”

“Mun kuma yi mamakin yadda sojojin saman Nijeriya suka ce ba su san da harin ba, mun yi mamaki yadda suka hau soma suka sako bam kan mutane. Mun yi mamakin yadda aka kona kusan mutum dari. Wannan hakika ya yi yawa.”

Ya ce, wannan babban sake ne da ya kama tun daga kan sojojin sama domin a cewarsa su ne ke da alhakin kula da yaƙin sama, da su kansu sojojin kasan hadi da ganin laifin gwamnati kan harin da ya farun.

Ya yi kira ga gwamnati da ta gaggauta kafa kwamiti domin binciko ta yadda lamarin ya faru da har aka kashe mutane kusan 100.

“Muna neman su sanar da mu yadda aka ƙona mana masu maulidi a jirgin sama. Mun ji zafi matuka. Gwamnati tana nan tana kallo aka yi wannan abun a gabanta, don haka muna neman ta biya diyya na mutanenmu masu maulidi,” Sheikh Dahiru ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron SGI Na Gudana Kan Sauyin Yanayi Karo Na 28

Next Post

Jami’in Diflomasiyyar Falasdinu: PA Ta Godewa Kasar Sin Bisa Aikewa Da Agaji Ga ’Yan Gaza Cikin Sa’o’in Bukata

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

8 hours ago
Bauchi
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
Jami’in Diflomasiyyar Falasdinu: PA Ta Godewa Kasar Sin Bisa Aikewa Da Agaji Ga ’Yan Gaza Cikin Sa’o’in Bukata

Jami’in Diflomasiyyar Falasdinu: PA Ta Godewa Kasar Sin Bisa Aikewa Da Agaji Ga ’Yan Gaza Cikin Sa’o’in Bukata

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.