ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

by Abubakar Abba and Sulaiman
12 months ago
IFAD

Gwamnatin Tarayya tare da hadin gwiwar Gidauniyar Bunkasa Aikin Gona ta Kasa da Kasa (IFAD)na kokarin samar da wata manhajar zamani ga manoman Nijeriya, domin fara tantance su.

Hadakar, za ta bayar da damar yi wa manoman kasar nan rijista, wacce za ta bayar da damar gano kowanne manomi da gonakinsa da irin kasar noman da yake amfani da ita da kuma irin nau’in amfanin gonar da yake nomawa.

  • Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
  • 2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Haka zalika, za a shigo da sashen samar da bayanai da kuma hukumar da ke rajistar katin dan kasa (NIMC), domin gudanar da wannan aiki.

ADVERTISEMENT

Manhajar za kuma ta sama wa manoman kasar damar samun kudade a matsayin rance ba tare da wani bata lokaci ba daga wajen gwamnati.

Kazalika, ana sa ran aikin zai tattaro daukacin manoman da ke kasar da kuma samun bayanan kafatanin manoman da ke jihohi 36 na wannan kasa, ciki har da babban birnin tarayyar Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

A jawabinsa a wajen taron kaddamar da tsarin tattaunawa kan shirin yin amfani da fashar zamani na samar da yin rjitsar ta manoman kasar (NDFR), wadda aka gudanar a babban birnin tarayyar Abuja, Babban Sakatare a Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Dakta Marcus Ogunbiyi, ya bayyana cewa; sabon tsarin zai taimaka matuka, wajen rage duk wani matsayi da manoman kasar suke ciki, musamman manoman da ba su mallaki wata gona ba.

“Za mu tabbatar mun yi rijistar sunayen manoman kasar da kuma gonakinsu, sannan kuma ba wai kawai yin rijistar ba, har da irin nau’in amfanin da suke nomawa da kuma nau’in irin kasar da ke gonakin nasu,” in ji Marcus.

Dakta Marcus ya kara da cewa, babu wata gona da ba ta da manomi, amma akwai manoma da dama da ba su mallaki gonaki ba.

“Idan mun yi wa manoman rijistar, za mu raba musu Kati kai tsaye da kuma wani Katin na manhajar zamani, domin a rika yin aiki da manoman kai tsaye ta yadda za a iya saurin gano kowane manomi a cikin sauki,” a cewar Marcus.

Ya ci gaba da cewa, hakan zai bayar da damar samun adana bayanansu kai tsaye da ya kunshi na sheda, musamman domin su rika samun taimakon daga wurin gwamnat da ya hada da samun rancen kudin yin noma.

Markus ya bayyana cewa, domin samun cin nasarar wannan aiki, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abincii, ta dauki wasu matakai domin samun bayanan manoman kasar tare da adana bayannan nasu.

Ya ci gaba da cewa, guda daga cikin dabarun aikin shi ne, na yin hadaka da hukumar da ke rajistar katin dan kasa (NIMC), musamman domin wanzar da wannan aiki na yi wa manoman rijista da kuma tattara bayanansu, domin tabbatar da ganin kowane manomi, an sanya shi a cikin tsarin.

Ita kuwa a nata jawabin, Daraktar IFAD a kasar nan, Madam Dede Ahoefa Ekoue ta bayyana cewa, sashen samar da abinci na Majalisar Dinkin Duniya, na alfaharin kasancewa cikin wannan sabon shirin.

“Gundunmawarmu ita ce, kokarin samun damar jawo sauran abokan hadaka na gwamnati da kuma masu kamfanoni masu zaman kansu, ta yadda za su zuba kudade tare, domin taimaka wa kokarin gwamnatin kasar, na yin rijistar manoman kasar,“ in ji Dede.

Madam Dede ta kara da cewa, koda-yake a baya, an yi irin wannan kokarin, amma ya kamata a ci gaba da wannan shirin, duba da muhimmancin da yake da shi.

“A yanzu, gwamnatin kasar ta samar mana da wata alkibla da kuma umartar daukacin masu ruwa da tsaki a fannin aikin noman kasar, domin a yi aiki tare,“ in ji ta.

Ta sanar da cewa, irin wannan aikin ne muke yi da sauran abokan hadaka kamar irin su; Bankin Raya Nahiyar Afrika, Hukumar Bunkasa Samar da Wadataccen Abinci, Bankin Duniya, Tarayyar Turai, Bankin Bunkasa Musulunci da kuma Gwamnatin Burtaniya.

Kazalika, ta sanar da cewa; babbin abin shi ne, ta hanyar yin aiki da kungiyoyin manoman kasar nan, domin su ne za su amfana da aikin.

Madam Dede ta ci gaba da cewa, hukumar ta IFAD, na matukar farin cikin jawo abokan hadaka da sauran sassan ma’aikatun gwamnati da sauran hukomomin gwamnatin kasar, domin tafiya tare cikin aikin.

Ta yi nuni da cewa, wannan aiki zai kasance tamkar samar da wani sauyi ne na ci gaba ga fanin aikin noman kasar.

Shi ma a nasa jawabin, Darakan kungiyar kasa da kasa ta Heifer da ke aiki a kasar nan, Dakta Lekan Tobe ya bayyana babban muhimancin da ke tattare da aikin, musamman ta hanyar yin hadaka.

Ya sanar da cewa, wannan aikin na daga cikin wasu shawarwarin da aka bayar a baya, wanda gwamnatin kasar nan ta yi hadaka da nufin yin amfani da fasahar zamani, domin a kara samar da wadataccen abinci a kasar.

IFAD
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
IFAD
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.