ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

by Abubakar Abba and Sulaiman
1 year ago
IFAD

Gwamnatin Tarayya tare da hadin gwiwar Gidauniyar Bunkasa Aikin Gona ta Kasa da Kasa (IFAD)na kokarin samar da wata manhajar zamani ga manoman Nijeriya, domin fara tantance su.

Hadakar, za ta bayar da damar yi wa manoman kasar nan rijista, wacce za ta bayar da damar gano kowanne manomi da gonakinsa da irin kasar noman da yake amfani da ita da kuma irin nau’in amfanin gonar da yake nomawa.

  • Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
  • 2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Haka zalika, za a shigo da sashen samar da bayanai da kuma hukumar da ke rajistar katin dan kasa (NIMC), domin gudanar da wannan aiki.

ADVERTISEMENT

Manhajar za kuma ta sama wa manoman kasar damar samun kudade a matsayin rance ba tare da wani bata lokaci ba daga wajen gwamnati.

Kazalika, ana sa ran aikin zai tattaro daukacin manoman da ke kasar da kuma samun bayanan kafatanin manoman da ke jihohi 36 na wannan kasa, ciki har da babban birnin tarayyar Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

A jawabinsa a wajen taron kaddamar da tsarin tattaunawa kan shirin yin amfani da fashar zamani na samar da yin rjitsar ta manoman kasar (NDFR), wadda aka gudanar a babban birnin tarayyar Abuja, Babban Sakatare a Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Dakta Marcus Ogunbiyi, ya bayyana cewa; sabon tsarin zai taimaka matuka, wajen rage duk wani matsayi da manoman kasar suke ciki, musamman manoman da ba su mallaki wata gona ba.

“Za mu tabbatar mun yi rijistar sunayen manoman kasar da kuma gonakinsu, sannan kuma ba wai kawai yin rijistar ba, har da irin nau’in amfanin da suke nomawa da kuma nau’in irin kasar da ke gonakin nasu,” in ji Marcus.

Dakta Marcus ya kara da cewa, babu wata gona da ba ta da manomi, amma akwai manoma da dama da ba su mallaki gonaki ba.

“Idan mun yi wa manoman rijistar, za mu raba musu Kati kai tsaye da kuma wani Katin na manhajar zamani, domin a rika yin aiki da manoman kai tsaye ta yadda za a iya saurin gano kowane manomi a cikin sauki,” a cewar Marcus.

Ya ci gaba da cewa, hakan zai bayar da damar samun adana bayanansu kai tsaye da ya kunshi na sheda, musamman domin su rika samun taimakon daga wurin gwamnat da ya hada da samun rancen kudin yin noma.

Markus ya bayyana cewa, domin samun cin nasarar wannan aiki, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abincii, ta dauki wasu matakai domin samun bayanan manoman kasar tare da adana bayannan nasu.

Ya ci gaba da cewa, guda daga cikin dabarun aikin shi ne, na yin hadaka da hukumar da ke rajistar katin dan kasa (NIMC), musamman domin wanzar da wannan aiki na yi wa manoman rijista da kuma tattara bayanansu, domin tabbatar da ganin kowane manomi, an sanya shi a cikin tsarin.

Ita kuwa a nata jawabin, Daraktar IFAD a kasar nan, Madam Dede Ahoefa Ekoue ta bayyana cewa, sashen samar da abinci na Majalisar Dinkin Duniya, na alfaharin kasancewa cikin wannan sabon shirin.

“Gundunmawarmu ita ce, kokarin samun damar jawo sauran abokan hadaka na gwamnati da kuma masu kamfanoni masu zaman kansu, ta yadda za su zuba kudade tare, domin taimaka wa kokarin gwamnatin kasar, na yin rijistar manoman kasar,“ in ji Dede.

Madam Dede ta kara da cewa, koda-yake a baya, an yi irin wannan kokarin, amma ya kamata a ci gaba da wannan shirin, duba da muhimmancin da yake da shi.

“A yanzu, gwamnatin kasar ta samar mana da wata alkibla da kuma umartar daukacin masu ruwa da tsaki a fannin aikin noman kasar, domin a yi aiki tare,“ in ji ta.

Ta sanar da cewa, irin wannan aikin ne muke yi da sauran abokan hadaka kamar irin su; Bankin Raya Nahiyar Afrika, Hukumar Bunkasa Samar da Wadataccen Abinci, Bankin Duniya, Tarayyar Turai, Bankin Bunkasa Musulunci da kuma Gwamnatin Burtaniya.

Kazalika, ta sanar da cewa; babbin abin shi ne, ta hanyar yin aiki da kungiyoyin manoman kasar nan, domin su ne za su amfana da aikin.

Madam Dede ta ci gaba da cewa, hukumar ta IFAD, na matukar farin cikin jawo abokan hadaka da sauran sassan ma’aikatun gwamnati da sauran hukomomin gwamnatin kasar, domin tafiya tare cikin aikin.

Ta yi nuni da cewa, wannan aiki zai kasance tamkar samar da wani sauyi ne na ci gaba ga fanin aikin noman kasar.

Shi ma a nasa jawabin, Darakan kungiyar kasa da kasa ta Heifer da ke aiki a kasar nan, Dakta Lekan Tobe ya bayyana babban muhimancin da ke tattare da aikin, musamman ta hanyar yin hadaka.

Ya sanar da cewa, wannan aikin na daga cikin wasu shawarwarin da aka bayar a baya, wanda gwamnatin kasar nan ta yi hadaka da nufin yin amfani da fasahar zamani, domin a kara samar da wadataccen abinci a kasar.

IFAD
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
IFAD
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.