• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kaduna: Muna Neman Afuwar Kisan Masu Maulidi – Hafsan Sojin Kasa

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kaduna: Muna Neman Afuwar Kisan Masu Maulidi – Hafsan Sojin Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hafsan hafsoshin sojin kasa, Janar Taoreed Lagbaja ya mika sakon neman afuwa daga al’ummar Jihar Kaduna, sakamakon harin bam din da sojoji suka kai wanda ya yi sanadiyar rasa rayukan sama da mutane 85.

Yayin da yake jawabi cikin alhini lokacin da ya kai ziyara kauyen Tudun Biri da ke Karamar Hukumar Igabi, Janar Lagbaja ya bayyana bakin cikinsa da lamarin.

  • Kotu Ta Yanke Wa Sojan Da Ya Kashe Sheikh Bagoni Aisami Hukuncin Kisa
  • Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai

Kakakin rundunar Janar Onyema Nwachukwu, ya ce hafsan hafsoshin ya bayyana cewar a ‘yan makonnin da suka gabata, ‘yan ta’adda sun kutsa kai a wannan yankin, abin da ya sa sojoji suka kaddamar da hare-hare, kuma sakamakon haka ne na’urarsu ta gano taron dandazon mutane a wurin Maulidin da aka kai musu hari cikin kuskure.

Lagbaja ya ce abin da ya sa ya ziyarci kauyen da kansa shi ne ya jajanta wa al’ummar yankin kan faruwar lamarin.

Hafsan ya ce ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin domin gano inda aka samu kuskure, domin taimaka musu wajen inganta ayyukansu nan gaba.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

A nasa jawabi, Hakimin Rigasa, Aminu Idris ya ce duk da zafin kisan da suke ji, sun gamsu da yadda rundunar sojin ta nuna damuwa da kuma amsa kuskuren da jami’anta suka yi dangane da kai harin, yayin da ya bukaci kai dauki ga iyalan wadanda abun ya shafa.

Hakimin, ya yi karin hasken cewar cikin wadanda harin ya rutsa da su har da Kiristocin da ke zaune a garin.

Daga bisani Janar Lagbaja ya jagoranci tawagarsa zuwa asibitin Barau Dikko domin duba wadanda suka jikkata.

Tuni kungiyoyi da daidaikun mutane suka shiga nuna alhininsu kan harin bam din da ya yi sanadin mutuwar masu taron Mauludin.

Sai dai lamarin ya dauki zafi a kafafen sada zumunta, inda mutane ke ganin wannan lamari a matsayin babban kuskure kuma dole ne a dauki mataki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HariKadunaSojojiTaron MaulidiTudun Biri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Yanke Wa Sojan Da Ya Kashe Sheikh Bagoni Aisami Hukuncin Kisa

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

14 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

19 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

20 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da É—umi-É—uminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

LABARAI MASU NASABA

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.