• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Yiwuwar Gwamnati Ta Kara Yawan Kasafin Kudin 2024 – Ministan Kudi

by Abubakar Abba
2 years ago
Ministan Kudi

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa mai yuwuwa ta sake dawo wa gaban hadakar majalisar kasar don ta nemi amincewar ‘yan majalisar tarayya a kan kara yawan kasafin kudin 2024, amma idan ta samu kari kudaden shiga da ta ayyana za ta samu.

A makonnin da suka gabata ne, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gabatar wa majalisar kudurin kasafin kudin 2024, wanda ya kai naira tirliyan 27.5.

  • Kwamitin Majalisar Dattawa Ya Nemi A Karawa Ma’aikatar Yaɗa Labarai Kudi Kan Kasafin 2024
  • Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Raba Fasahohinta Na Bunkasa Tattalin Arziki Na Zamani Da Sauran Kasashe Masu Tasowa

Ministan kudi da tattalin arziki, Mista Wale Edun shi ya bayyana hakan a lokacin da yake kare kasafin kudin a gaban kwamitin majalisa da ke kula da harkokin kudade.

Edun ya kuma shaida wa ‘yan kwamitin cewa, an samu gagarumin ci gaba a fannin tara kudaden shiga na kasar nan a ‘yan watan da suka gabata, inda ya kara da cewa, kudaden shigar na gwamnatin sun karu.
Ya ci gaba da cewa, gwamnatin na yin dubi a kan yadda za ta kara hanzarta kashe kudin da ta ware a cikin kasafin kudin 2024.

A cewar Edun, kudin shigar ya kai kashi biyar a cikin dari, wanda hakan ya nuna wani kwarin gwiwa kan samun kudaden musaya duk da cewa darajar naira ya ragu, sannan akwai sauran bashin da ake bin gwamnatin wanda ya kai kimanin dala 46.

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

Ya kara da cewa bashin da gwamnatin ta biya ya kai kashi 18 a cikin dari, inda ya kai kasa da abin da aka ware a cikin kasafin kudin na badi.
Ministan ya sanar da cewa gibin da aka samu a kasafin kudin ana sa ran zai ragu daga naira tiriliyan 13.7 zuwa naira tirilyan 9.2.

Ya sanar da cewa, yawan kudin da za a amso bashi a cikin kasafin kudin ya ragu daga kashi 6.1 a cikin dari zuwa kashi 3.9.

Edu ya kara da cewa wannan kasafin kudi ne ta sake sabunta fata wannan kasa shi ya sa mai girma shugaban kasa ya aiwatar da shi cikin lokaci.

A nasa bangaren shugaban kwamtin harkokin kudade, Sanata Sani Musa ya bayyana cewa Nijeriya na cikin wani mawuyacin hali a fannin tattalin arziki, musamman a bangaren rashin aikin yi.

Sai dai, Musa ya ce yana da yakinin cewa, gwamnatin Shugaba Tinubu na kan yin dukkanin mai yuwa don lalubo da mafita a kan wannan kalubalen.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma
Labarai

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
tinubu
Labarai

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Next Post
Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Yi Watsi Da Buƙatar Sakin Nnamdi Kanu

Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Yi Watsi Da Buƙatar Sakin Nnamdi Kanu

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.