ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamitin Majalisar Dattawa Ya Nemi A Karawa Ma’aikatar Yaɗa Labarai Kudi Kan Kasafin 2024

by Sulaiman
3 years ago
Dattawa

Kwamitin Majalisar Dattawa Mai Lura da Harkokin Yaɗa Labarai, ya nuna rashin amincewa dangane da ƙarancin kuɗaɗen da kwamitin ya ce Gwamnatin Tarayya ta ware wa Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da kai, a Kasafin 2024.

Shugaban kwamitin, Sanata Kenneth Eze ne ya nuna damuwa da rashin amincewa dangane da ƙarancin kuɗaɗen, a lokacin da Ministan Yaɗa Labarai, Alhaji Mohammed Idris ya bayyana a gaban kwamitin, domin ya kare kasafin ma’aikatarsa, a ranar Talata, a Abuja.

  • Jamhuriyar Nijar Za Ta Fara Fitar Da Danyen Mai A Watan Janairu
  • Na Samu Farin Ciki Sosai A Farkon Fara Rubutuna – Fauziyya

“Haba jama’a, ai waɗannan kuɗaɗe cikin cokali bai yiwuwa a ce da su kaɗai za a yi amfani har a samu biyan buƙatar yada manufofin ƙasarmu. Muddin waɗannan kuɗaɗen ne aka ware wa wannan ma’aikatar, to ba inda za mu iya cimma gaci. Ta yaya za a iya wayar da kan jama’a ta hanyar yaɗa labarai da kyawawan manufofi da waɗannan kuɗaɗe ƙalilan?

ADVERTISEMENT

“Ma’aikatar Yaɗa Labarai fa wuri ne mai muhimmancin da wajibi ne a yi wa wurin riƙon kazar kuku, ba riƙon sakainar kashi ba. Ina magana idan har fa ana so a samu biyan buƙatar samun nasarar Ajandar Saidaita Nijeriya da mu ke magana, to dole ma’aikatar yaɗa labarai ce a sahun gaba.

“Wannan ma’aikata ce za ta kasance mai haska wa ƙasar nan fitilar kyakkyawar ɗabi’un jama’ar ta, kuma akwai wawakeken giɓi tsakanin gwamnati da jama’a, wanda wannan ma’aikatar ce tilas za ta iya cike giɓin,” inji sanatan.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Na duba a cikin kasafin, amma ban ga ko sisi da za a kashe a Hukumar Kula da Jaridu ba, ban ga Hukumar APCON ba, kuma ban ga kasafin wasu hukumomin da ke ƙarƙashin wannan ma’aikata ba.

“Shin gwamnati na so ta shaida mana cewa an rushe waɗannan hukumomin kenan, yadda har za su iya aiki ko ba ma’aikata a cikin su?

“Wa zai biya albashin su? Watannin baya ba da daɗewa ba fa aka naɗa wa hukumomin sabbin Manyan Daraktoci da Manyan Sakatarori.

Kenneth ya ci gaba da cewa, “Mai Girma Minista, wannan batu ne fa mai muhimmanci ga wannan kwamiti, kuma tabbas za mu duba wannan lamari.”

A nasa bayanin, Minista Idris ya shaida wa sanatocin cewa za a ƙaddamar da Shirin Cusa Ɗa’a, Kishin Ƙasa da Kyawawan Ɗabi’u (NVC) cikin 2024.

Ya ce akwai gagarimin aiki a gaban ma’aikatar sa wajen tabbatar da samun nasarar shirin cusa ɗa’a da kishin ƙasa, wanda Naira biliyan 1 da aka ware wa ma’aikatar sa, a matsayin kuɗaɗen gudanar da manyan ayyuka, ko kusa ba za su wadata ba.

Dattawa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Gana Da Manyan Shugabannin Kasar Vietnam

Shugaba Xi Ya Gana Da Manyan Shugabannin Kasar Vietnam

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.