• English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Musawa Ta Kudiri Aniyar Kafa Gidan Tarihi Da Gidan Wasanni Na Ƙasa A Abuja

Ta yi kukan ƙanƙantar Kasafin Kuɗin ma'aikatarta

by Sulaiman
2 years ago
Musawa

Ma’aikatar Fasaha, Al’adu Da Basira, ta ƙudiri aniyar  Gina birnin Basira da za a gina Gidan Tara Kayan Tarihi da kuma Gidan Wasannip a Abuja.

Ministar ma’aikatar, Barista Hannatu Musa Musawa, ita ce ta bayyana hakan a lokacin da ta gabatar da Kasafin Kuɗin ma’aikatar na shekarar 2024 a gaban Kwamitin Fasaha, Al’adu Da Tattalin Arzikin Basira na Majalisar Dattawa a ranar Alhamis a Majalisar Tarayya a Abuja.

  • Tinubu Ya Zama Gwarzon Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP
  • Kamfanonin Jirage Za Su Fara Biyan Tarar Jinkirta Tashi Da Soke Tafiya

A cikin sanarwar da Hadimarta ta Musamman kan Yaɗa Labarai, wato Nneka Ikem Anibeze, ta fitar, an ruwaito Barista Hannatu ta na cewa kafa wuraren guda biyu ya na daga cikin manyan muhimman ayyukan da ma’aikatar ta sanya a gaba da nufin samar da aikin yi, ba kurum ga masu ayyukan fasaha ba har ma ga sauran ‘yan Nijeriya baki ɗaya.

A cewar ministar, cimma wannan nasarar zai yiwu ne idan har an samu amincewa da Kasafin Kuɗin shekarar 2024 daga Majalisar Dattawa.

Haka kuma ministar ta yi la’akari da cewa kuɗin da aka kasafta wa ma’aikatar ta sun yi kaɗan matuƙa, sannan ta yi kira ga Kwamitin na Majalisar Dattawa da ya ƙara yawan kuɗin a cikin Kasafin shekarar 2024 ɗin.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Barista Hannatu ta ce: “Kuɗin da aka kasafta wa Ma’aikatar sun yi kaɗan matuƙar gaske, wanda ya sa ba za mu iya cimma wani abin a zo a gani ba idan ba a bada kuɗin da su ka dace ba.

“Nasarar da wannan Ma’aikatar za ta cimmawa gagaruma ce idan mun yi abin da ya kamata, don haka mu na so mu ga abin da za mu iya yi a matakin majalisa domin bai wa ma’aikatar irin kasafin kuɗi da ya kamata tare da goyon bayan da mu ke buƙata don cimma burin mu a tsarin da gwamnati ta yi, wato domin mu cimma muradun Sabuwar Alƙiblar Saisaita Ƙasa ta mai girma Shugaban Ƙasa.”

A bisa Sabuwar Alƙiblar Saisaita Ƙasa ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu dai, wannan ma’aikatar ta ƙudiri aniyar kawo gudunmawar kuɗin shiga da ya kai naira biliyan 100 ga tattalin arzikin ƙasar nan zuwa shekarar 2030 tare kuma da kafa manyan ayyuka da su ka haɗa da gina Gidan Wasanni na Ƙasa da Gidan Tara Kayan Tarihi na Ƙasa a birnin Abuja, da sauran su.

Tun da farko, sai da Barista Hannatu Musa Musawa ta nanata aniyar ma’aikatar ta ta sake fasalin Nijeriya ta hanyoyin waɗannan ayyukan da ta ke son ta aiwatar.

Ta yi bayani kan muhimmanci da alfanun da ke tattare da Tattalin Arzikin Basira da kuma gundarin ayyukan da aka rataya wa Ma’aikatar waɗanda su ka haɗa da janyo zuba jari, haɓaka al’adu da adana su, da sauran su, kamar yadda sashe na 21 na Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999 ya tanadar.

Ta ce, “Mun lissafa Alamomin Manyan Nasarorin da ma’aikatar ta ke so ta cimmawa kuma a shirye mu ke mu ga mun cimma dukkan nasarorin da mu ka ɗora wa kan mu.

“Wannan sabuwar ma’aikata ce wadda kuma ta ke so ta yi ƙoƙarin samar da aikin yi sannan kuma ta samar da Tsarin Kare Haƙƙin Mallaka wanda zai kula da sha’anin al’adu da ƙirƙira a Nijeriya. Saboda haka, wannan abu ne wanda ke buƙatar cikakkiyar ɗaukar nauyi ta fuskar kuɗi.”

A nasa jawabin, Shugaban Kwamitin Fasaha, Al’adu Da Tattali Arzikin Basira na Majalisar Dattawa, Sanata Mohammed Ogoshi Onawo, ya yaba wa ministar saboda sababbin al’amuran da ta bijiro da su, wato kafa Gidan Tara Kayan Tarihi da kuma Gidan Wasanni a Abuja, kuma ya bayyana cewa sake duba kasafin kuɗin zai taimaka mata wajen gudanar da aikin ta da kyau kuma ta cimma burukan ma’aikatar.

Ya ce: “Wannan kwamiti zai so mu riƙa haɗuwa da juna a kai a kai a cikin shekara da za a yi nan gaba domin a samu daidaito kuma a tabbatar da haɗin gwiwa da Majalisar Dattawa.”

Wani memba a kwamitin, Sanata Ede Dafinone, mai wakiltar Mazaɓar Delta ta Tsakiya, shi ma ya yi tsokaci kan ƙanƙantar kasafin kuɗin, ya bayyana damuwa kan yadda ma’aikatar za ta iya aiwatar da manyan ayyuka da wannan ɗan cikin cokalin kasafin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Next Post
Ministan Lantarki

Da Gangan Aka Cire Aikin Mambilla A Kasafin 2024 – Ministan Lantarki

LABARAI MASU NASABA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

November 10, 2025
FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.