• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kirsimeti: Farashin Abinci Da Sufuri Na Tashin Gwauron Zabi

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Kirsimeti: Farashin Abinci Da Sufuri Na Tashin Gwauron Zabi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana ‘yan kwanaki kadan za a gudanar da bukukuwan kiristimeti amma al’amurra na ci gaba da cunkushe wa ‘yan Nijeriya, musamman ganin hauhawar tsadar kayan abinci, tsadar harkokin rayuwa da kuma matsalar tattalin arziki gaba daya ya dakushe armashin bukukuwan kirismeti na bana.

Bincike ya nuna cewa, manyan matsalolin da suka haifar da matsalar tattalin arziki da al’ummar Nijeriya suka shiga ya hada matsalar tsaro da ta addabi sassan Nijeriya da kuma kulle iyakokin Nijeriya da gwamnati ta yi duk kuwa da an bayar da umarnin bude wasu iyakokin amma har yanzu ana dandanawa saboda tsadar kudin mota sakamakon janye tallafin man fetur da aka yi.

  • Majalisar Dokokin Sokoto Ta Amince Da Bukatar Gwamna Aliyu Na Kafa Jami’an Tsaron Jiha
  • Ashirye Muke Mu Amsa Duk Kura-kuran Da ‘Yan Jarida Suka Gano A Gwamnatinmu – Tinubu 

Iyalai da dama sun rage yadda suke cin abinci, wasu suna ci ne sau biyu ko sau daya a rana, wasu da dama kuma sun rasa yadda za su fuskanci rayuwa ganin dimbin matsalar tattalin arzikin da ake fuskanta kuma ga bukukuwan kiristime ya dunfaro, babu alamar za a yi bikin cikin armashi kamar yadda aka saba a shekarun baya.

A ta bakin wani malamin jami’a mai suna Dakta Ayobami Aderemi “Bama bukatar wani mai duba don ya gaya mana cewa, iyalai da dama na cikin tsananin matsain tattalin arziki wanda shugabanin kasa suka jefa su sakamakon tsare-tsaren su na tattalin arziki, ciki har da janye tallafin man fetur da aka yi ba tare da an samar da matakai na rage radadin da al’umma za su shiga ba.

A yanzu ana sayar da buhun shinkafar waje a kan N65,000 zuwa N70,000 yayin da ake sayar da ta gida a kan N50,000.

Labarai Masu Nasaba

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Aderemi ya ce, tabbas iyalai da dama ba za su bikin kiristimeti ba a cikin walwala ba, wannan yana kara nuna alamun irin matsala da karancin abinci da za a fuskanta a Nijeriya a nan gaba.

Bincike ya nuna cewa, yawancin ‘yan Nijeriya sun yanke shawarar gudanar da bukuwan kiristime a wuraren da suke ba kamar yadda suke yi a shekarun baya ba na tafiya grurunwan su na asalin, inda za ka ga magidanci tare da iyalansa sun hau mota zuwa garuruwasu amma a wannan shekara, saboda yadda kudin mota ya yi tashin gwauron zabi sakamakon karin farashin man fetur, mutane da dama da wakilinmu ya tattauna da su sun bayyana cewa ba inda za su tafi, “Zan zauna in yi bikin a Abuja saboda yadda kudin mota zuwa kudancin kasar nan ya tashi”, in ji wani magidanci da ya bukkaci mu sakaya sunansa.

Haka kuma wasu masu sana’ar dinki sun koka a kan yadda al’umma ba su yi dinki sosai ba kamar yadda suke yi a irin wannan lokacin a shekarun baya. Hassan Tela da ke babbar kasuwar Wuse a Abuja ya ce, a irin wanna lokacin a shekarun baya har kin karbar aiki suke yi amma a wannan shekarar mutane kalilan ne suka kawo musu dinki saboda matsalar tattalin arziki da ake fuskanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rayuwar ‘Yan Jari-bola Bayan Fatattakar Su A Abuja

Next Post

Shirin Bunkasa Noman Alkama: Da Gaske Rijiya Ta Bayar Guga Ta Hana A Yobe?

Related

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

3 hours ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

4 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

7 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

9 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

11 hours ago
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai
Labarai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

13 hours ago
Next Post
Shirin Bunkasa Noman Alkama: Da Gaske Rijiya Ta Bayar Guga Ta Hana A Yobe?

Shirin Bunkasa Noman Alkama: Da Gaske Rijiya Ta Bayar Guga Ta Hana A Yobe?

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.