ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Bunkasa Noman Alkama: Da Gaske Rijiya Ta Bayar Guga Ta Hana A Yobe?

by Muhammad Maitela
3 years ago
Noman

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Gwamnatin Tarayya ta sha bullo da muhimman shirye-shiryen farfado da harkokin noma, don inganta tattalin arziki, ayyukan yi tare da samar da isasshen abinci ga al’ummar kasa baki daya. Wanda a zahiri, wadannan muhimman shirye-shirye; idan an aiwatar da tsarin da yake a rubuce a takardu, hakan zai taimaka wajen kawo mafita ga wasu daga cikin wahalhalun da ‘Yan Nijeriya suke fuskanta na karancin abinci da hauhawar farashinsa.

Shirye-shiryen tallafa wa ayyukan da za su farfado da aikin noma tare da manoma sun hada da amfani da kungiyoyin manoma na kasa. Yayin da wani zubin ma’aikatar kula da aikin noma ta kasa ce ke daukar nauyin aiwatar da shirin, da zimmar ganin kwalliya ta biya kudin sabulu, amma daga bisani haka al’amarin zai wuce kamar hurawar iska.

  • Majalisar Dokokin Sokoto Ta Amince Da Bukatar Gwamna Aliyu Na Kafa Jami’an Tsaron Jiha
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Kasafin Biliyan 437.3 Na 2024

Duka wadannan tsare-tsaren daruruwan biliyoyin naira da gwamnatin tarayya ta fitar, ba su kai banten su ba, saboda yadda suka gamu da manya-manyan kurakurai, da suka hada da rashin kwararrun mutane masu amana, da za su aiwatar da tsarin zuwa ga manufar da aka tsara shi. Saboda ta hanyar kwararru ne kadai za a bi wajen zakulo manoma na gaskiya, wanda suka dauki harkar noma sana’a, kuma dadaddu a fagen, masu kishin da za su bayar da gudunmawa wajen goya wasu kanana a bayansu don nona musu hanyar da za ta taimaki gwamnati cimma wannan burin da ta saka a gaba.

Wannan babban gibin ne ya jawo wasu maras kishi da bara-gurbin ‘yan siyasa suka yi wa shirin mummunan targaden da ya kasa kai wa zangon da aka tsara zai isa. A sa’ilin da gwamnatin tarayya ta ware wadannan makudan kudade, a matsayin tallafa wa harkokin noma, tare da kyakkyawar manufa, amma ba tare da bibiyar yadda tsare-tsaren suke gudana ba, hakan ya bai wa maras kishi kasa da ci gaban al’umma damar watanda da dukiyar yan kasa- rijiya ta bayar guga ta hana.

A wani sabon yunkurinta na tunkarar matsalar karancin abinci, hauhawar farashin kayayyakin abinci da na masarufi, samar da ayyukan yi ga ‘yan kasa, Gwamnatin Tarayya a karkashin shugaban kasa Bola Ahamed Tinubu, ma’aikatar kula da ayyukan noma da samar da abinci, a makon da ya gabata ta kaddamar da bai wa manoma tallafin noman alkama na rani, na bana (2023/2024) a karkashin shirin bunkasa noma na National Agricultural Growth Scheme and Agro Pocket (NAGS-AP), wanda ake sa ran noma ton 1,250,000 na alkama a kowace shekara. Kuma bisa ga kididdigar masana, idan shirin ya gudana kamar yadda aka tsara shi, zai taimaka wajen rage hauhawar farashin kayayyakin abinci, samar da aikin yi, inganta habyoyin dogaro da kai tare da habaka tattalin arziki.

Da yake jawabi a lokacin kaddamar da shirin a kauyen Kadume dake karamar hukumar Hadejia a jihar Jigawa, Minista a Ma’aikatar Noma ta Nijeriya, Sanata Abubakar Kyari ya ce, “A wani bangare na shirin gwamnatin tarayya wajen tallafawa kimanin manoma 150,000 zuwa 250,000 na kashi 50 cikin dari domin samun damar noma tsakanin kadada (hekta) 200,000 zuwa 250,000 wajen cimma kudurin ta na tan 1,250,000 na alkama.”

Ministan ya kara da bayyana cewa, wannan shiri na noman rani wani muhimmin bangare ne na yunkurin bunkasa noma a karkashin shirin: AgroPocket (NAGS-AP), wanda aka samar da shi ta hanyar ranto dalar Amurka miliyan 134, tare da hadi da Bankin Raya Afirka (AfDB) a Nijeriya. Ya ce babban kudurin wannan Gwamnati shi ne farfado da harkokin noman shinkafa, masara, rogo da alkama, a kasar nan.

Har Ila yau, akwai yiwuwar Gwamnatin Tarayya ta fadada adadin yawan kananan manoman zuwa sama da 42,000 tare da baiwa kowane manomi daya tallafin kayan noma kashi 50 cikin dari daga adadin kudin da gwamnatin ta kashe wanda aka kiyasta kashe naira 361,000 ga kowace kadada daya.

A hannu guda kuma, Ministan ya bai wa jami’an tsaron fararen hula (NSCDC) da sauran jami’an tsaro su sanya ido sosai wajen dakile duk wani yunkurin karkatar da kayan, sabanin yadda aka tsara aiwatar dasu.

LEADERSHIP Hausa ta jiwo ra’ayoyin wasu daga cikin manoma a jihar Yobe dangane da raba wannan tallafin noman alkama, inda kaso mai yawa suka bayyana rashin gamsuwarsu dangane da yadda gwamnatin ta raba wannan tallafin.

Alhaji Ishak Muhammad, manomi a garin Gashu’a ta karamar hukumar Bade, ya ce ba shi da masaniya kan raba wannan tallafin noman alkama, ya kada baki ya ce, “Da kimanin karfe 8:00 na dare na ga sakon kar ta kwana ya shigo wayata (ban san wanda ya bayar da lambar wayata ba) sai daga baya wani mutum (ya boye sunan shi) ya kira ni, ya ce an tura maka sakon kayan noman alkama, gobe da safe ka tafi Filin Agric Katuzu. Bayan na zo aka ce na je na nuna sakon, daga baya mutumin ya karbi kayan, ya ba ni naira 25,000.”

Wakilinmu ya gano cewa, kowane manomi zai biya naira 180,000 sannan a bashi buhu 7 na takin zamani samfurin (NPK Nagari), lita 7 na takin zamani na ruwa, tare da magungunan kashe ciyawa da kwari 4, sai buhun irin alkama (50kg) guda biyu. Sannan kimanin kaso 70 cikin dari na wadanda aka tura wa sakon karbar kayan, manoman bogi ne, yayin da wasu daga cikin su kananan yara ne da ba su zarta shekara 12 zuwa 17 ba.

Alhaji Jabbi Mai-kanwa Gashu’a, shi ne Shugaban hadaddiyar kungiyar manoma ta jihar Yobe, ya bayyana cewa, “Ni ma haka na tsinci labarin ana raba kayan tallafin noman alkama a nan jihar Yobe; babu wanda ya tuntube mu a matsayinmu na shugabannin manoma- walau Gwamnatin Tarayya ko ta jihar Yobe kan batun. Amma iya fahimtarmu, kila al’amari ne wanda yan siyasa suka yi babakere a ciki.”

“Amma idan manoman gaskiya gwamnati take nema, ya dace a tuntube mu, saboda muna cikin wannan sabga ta noma sama da shekara 70. Duk da ba mu yi mamaki ba, amma abu ne mai wahala Gwamnatin Tarayya ta cimma burinta a wannan aiki.” Ya bayyana.

Har ila yau, wakilinmu a jihar Yobe ya tuntubi daya daga cikin masu hannu wajen aiwatar da raba kayan tallafin noman alkama, Alhaji Dayyabu Gashu’a, ta wayar tafi-da-gidanka inda ya ce ba zai ce komai ba kan batun. Wannan ya haifar da alamar tambayar, da gaske rijiya ta bayar da ruwa guga ta hana?

Noman
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Rahama, Jin Kai Da Hasken Manzon Allah (SAW)

Rahama, Jin Kai Da Hasken Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.