Ana ‘yan kwanaki kadan za a gudanar da bukukuwan kiristimeti amma al’amurra na ci gaba da cunkushe wa ‘yan Nijeriya, musamman ganin hauhawar tsadar kayan abinci, tsadar harkokin rayuwa da kuma matsalar tattalin arziki gaba daya ya dakushe armashin bukukuwan kirismeti na bana.
Bincike ya nuna cewa, manyan matsalolin da suka haifar da matsalar tattalin arziki da al’ummar Nijeriya suka shiga ya hada matsalar tsaro da ta addabi sassan Nijeriya da kuma kulle iyakokin Nijeriya da gwamnati ta yi duk kuwa da an bayar da umarnin bude wasu iyakokin amma har yanzu ana dandanawa saboda tsadar kudin mota sakamakon janye tallafin man fetur da aka yi.
- Majalisar Dokokin Sokoto Ta Amince Da Bukatar Gwamna Aliyu Na Kafa Jami’an Tsaron Jiha
- Ashirye Muke Mu Amsa Duk Kura-kuran Da ‘Yan Jarida Suka Gano A Gwamnatinmu – Tinubu
Iyalai da dama sun rage yadda suke cin abinci, wasu suna ci ne sau biyu ko sau daya a rana, wasu da dama kuma sun rasa yadda za su fuskanci rayuwa ganin dimbin matsalar tattalin arzikin da ake fuskanta kuma ga bukukuwan kiristime ya dunfaro, babu alamar za a yi bikin cikin armashi kamar yadda aka saba a shekarun baya.
A ta bakin wani malamin jami’a mai suna Dakta Ayobami Aderemi “Bama bukatar wani mai duba don ya gaya mana cewa, iyalai da dama na cikin tsananin matsain tattalin arziki wanda shugabanin kasa suka jefa su sakamakon tsare-tsaren su na tattalin arziki, ciki har da janye tallafin man fetur da aka yi ba tare da an samar da matakai na rage radadin da al’umma za su shiga ba.
A yanzu ana sayar da buhun shinkafar waje a kan N65,000 zuwa N70,000 yayin da ake sayar da ta gida a kan N50,000.
Aderemi ya ce, tabbas iyalai da dama ba za su bikin kiristimeti ba a cikin walwala ba, wannan yana kara nuna alamun irin matsala da karancin abinci da za a fuskanta a Nijeriya a nan gaba.
Bincike ya nuna cewa, yawancin ‘yan Nijeriya sun yanke shawarar gudanar da bukuwan kiristime a wuraren da suke ba kamar yadda suke yi a shekarun baya ba na tafiya grurunwan su na asalin, inda za ka ga magidanci tare da iyalansa sun hau mota zuwa garuruwasu amma a wannan shekara, saboda yadda kudin mota ya yi tashin gwauron zabi sakamakon karin farashin man fetur, mutane da dama da wakilinmu ya tattauna da su sun bayyana cewa ba inda za su tafi, “Zan zauna in yi bikin a Abuja saboda yadda kudin mota zuwa kudancin kasar nan ya tashi”, in ji wani magidanci da ya bukkaci mu sakaya sunansa.
Haka kuma wasu masu sana’ar dinki sun koka a kan yadda al’umma ba su yi dinki sosai ba kamar yadda suke yi a irin wannan lokacin a shekarun baya. Hassan Tela da ke babbar kasuwar Wuse a Abuja ya ce, a irin wanna lokacin a shekarun baya har kin karbar aiki suke yi amma a wannan shekarar mutane kalilan ne suka kawo musu dinki saboda matsalar tattalin arziki da ake fuskanta.