ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kirsimeti: Farashin Abinci Da Sufuri Na Tashin Gwauron Zabi

by Bello Hamza
3 years ago
Kirismeti

Ana ‘yan kwanaki kadan za a gudanar da bukukuwan kiristimeti amma al’amurra na ci gaba da cunkushe wa ‘yan Nijeriya, musamman ganin hauhawar tsadar kayan abinci, tsadar harkokin rayuwa da kuma matsalar tattalin arziki gaba daya ya dakushe armashin bukukuwan kirismeti na bana.

Bincike ya nuna cewa, manyan matsalolin da suka haifar da matsalar tattalin arziki da al’ummar Nijeriya suka shiga ya hada matsalar tsaro da ta addabi sassan Nijeriya da kuma kulle iyakokin Nijeriya da gwamnati ta yi duk kuwa da an bayar da umarnin bude wasu iyakokin amma har yanzu ana dandanawa saboda tsadar kudin mota sakamakon janye tallafin man fetur da aka yi.

  • Majalisar Dokokin Sokoto Ta Amince Da Bukatar Gwamna Aliyu Na Kafa Jami’an Tsaron Jiha
  • Ashirye Muke Mu Amsa Duk Kura-kuran Da ‘Yan Jarida Suka Gano A Gwamnatinmu – Tinubu 

Iyalai da dama sun rage yadda suke cin abinci, wasu suna ci ne sau biyu ko sau daya a rana, wasu da dama kuma sun rasa yadda za su fuskanci rayuwa ganin dimbin matsalar tattalin arzikin da ake fuskanta kuma ga bukukuwan kiristime ya dunfaro, babu alamar za a yi bikin cikin armashi kamar yadda aka saba a shekarun baya.

ADVERTISEMENT

A ta bakin wani malamin jami’a mai suna Dakta Ayobami Aderemi “Bama bukatar wani mai duba don ya gaya mana cewa, iyalai da dama na cikin tsananin matsain tattalin arziki wanda shugabanin kasa suka jefa su sakamakon tsare-tsaren su na tattalin arziki, ciki har da janye tallafin man fetur da aka yi ba tare da an samar da matakai na rage radadin da al’umma za su shiga ba.

A yanzu ana sayar da buhun shinkafar waje a kan N65,000 zuwa N70,000 yayin da ake sayar da ta gida a kan N50,000.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Aderemi ya ce, tabbas iyalai da dama ba za su bikin kiristimeti ba a cikin walwala ba, wannan yana kara nuna alamun irin matsala da karancin abinci da za a fuskanta a Nijeriya a nan gaba.

Bincike ya nuna cewa, yawancin ‘yan Nijeriya sun yanke shawarar gudanar da bukuwan kiristime a wuraren da suke ba kamar yadda suke yi a shekarun baya ba na tafiya grurunwan su na asalin, inda za ka ga magidanci tare da iyalansa sun hau mota zuwa garuruwasu amma a wannan shekara, saboda yadda kudin mota ya yi tashin gwauron zabi sakamakon karin farashin man fetur, mutane da dama da wakilinmu ya tattauna da su sun bayyana cewa ba inda za su tafi, “Zan zauna in yi bikin a Abuja saboda yadda kudin mota zuwa kudancin kasar nan ya tashi”, in ji wani magidanci da ya bukkaci mu sakaya sunansa.

Haka kuma wasu masu sana’ar dinki sun koka a kan yadda al’umma ba su yi dinki sosai ba kamar yadda suke yi a irin wannan lokacin a shekarun baya. Hassan Tela da ke babbar kasuwar Wuse a Abuja ya ce, a irin wanna lokacin a shekarun baya har kin karbar aiki suke yi amma a wannan shekarar mutane kalilan ne suka kawo musu dinki saboda matsalar tattalin arziki da ake fuskanta.

Kirismeti
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Shirin Bunkasa Noman Alkama: Da Gaske Rijiya Ta Bayar Guga Ta Hana A Yobe?

Shirin Bunkasa Noman Alkama: Da Gaske Rijiya Ta Bayar Guga Ta Hana A Yobe?

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.